Yobe
Yobe jiha ce daga cikin jerin jihohin shiyyar Arewa Maso Gabashin Najeriya. Tana da yawan kasa kimanin murabba'in kilomita 45,502 da yawan jama’a miliyan ɗaya da dubu ɗari huɗu da sha ɗaya da ɗari huɗu da tamanin da ɗaya (a ƙidayar yawan jama'a ta shekarar 1991). Babban birnin jihar shi ne Damaturu. Mai Mala Buni shi ne gwamnan jihar tun zaɓen shekara ta 2015 zuwa yau. Mataimakin gwamnan shi ne Idi Barde Gubana. Jihar dai tana da shiyyoyi guda uku: shiyyar gabas, kudu da kuma arewa. 'yan majalisar Dattijan jihar su ne: Ahmed Ibrahim Lawan mai wakiltar shiyyar arewaci, Bukar Abba Ibrahim Gaidam shiyyar gabashi da , Mohammed Bomai shiyyar kudanci.
![]() | |||||
---|---|---|---|---|---|
|
|||||
| |||||
Suna saboda | Komadugu Yobe | ||||
Wuri | |||||
| |||||
Ƴantacciyar ƙasa | Najeriya | ||||
Babban birni | Damaturu | ||||
Yawan mutane | |||||
Faɗi | 3,294,137 (2016) | ||||
• Yawan mutane | 72.4 mazaunan/km² | ||||
Harshen gwamnati | Turanci | ||||
Labarin ƙasa | |||||
Yawan fili | 45,502 km² | ||||
Wuri a ina ko kusa da wace teku | Komadugu Yobe | ||||
Sun raba iyaka da | |||||
Bayanan tarihi | |||||
Mabiyi | Jihar Borno | ||||
Ƙirƙira | 27 ga Augusta, 1991 | ||||
Tsarin Siyasa | |||||
Majalisar zartarwa |
executive council of Yobe State (en) ![]() | ||||
Gangar majalisa |
Yobe State House of Assembly (en) ![]() | ||||
Bayanan Tuntuɓa | |||||
Kasancewa a yanki na lokaci | |||||
Lamba ta ISO 3166-2 | NG-YO | ||||
Wasu abun | |||||
| |||||
Yanar gizo | yobestategov.com |
Jihar Yobe tana da iyaka da jihohi huɗu, su ne: Bauchi, Borno, Gombe da kuma Jigawa. Tana kuma da iyaka da jamhuriyar Nijar.
TarihiGyara
An ƙirƙiri jihar Yobe ne a ranar 27 na watan Agustan 1991. An ciro ta ne daga jihar Borno a zamanin mulkin Ibrahim Badamasi Babangida kuma an yi hakan ne don a sauƙaƙa sha'anin tafiyar da mulki a yankin. Ranar 14 ga watan Mayu 2013, Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya rattaba dokar ta ɓaci a jihar Yobe da Borno da kuma Adamawa. Saboda harin ta'addanci na kungiyar Boko Haram. Karkashin Abubakar Shekau, shugaban ƙungiyar ta Boko Haram, haifaffen ƙauyen Shekau ne na jihar Yobe.
Kananan hukumomiGyara
Yobe tana da ƙananan hukumomi goma sha bakwai wadanda suka haɗa da:
HarsunaGyara
Waɗannan su ne harsunan mutanen Jihar da kuma ƙananan hukumomin da ake samun su:[1]
Kananan Hukumomi | Harsuna |
---|---|
Bade | Bade; Duwai |
Bursari | Fulbe Bade |
Damaturu | Kanuri; Fulani |
Fika | Karaikarai; Ngamo; Fulani Bolewa |
Fune | Fulani,Abore |
Geidam | Kanuri |
Gujba | Fulani,Kanuri, |
Gulani | Maaka, Fulani |
Jakusko | Fulani, Bade, |
Nangere | Karaikarai, Fulani, |
Nguru | Kanuri; Hausa; Bade |
Potiskum | Karaikarai; Ngizim; Bolewa |
Tarmuwa | Fulani, kanuri |
Yunusari | Kanuri, Fulani |
Yusufari | Kanuri, Fulani |
Machina | Mangawa |
Sauran harsunan da ake samu a jihar Yobe sun hada da Baburawa, Mangawa da kuma Zarmawa.[1]
Hotunan wasu sassa na YobeGyara
Fitattun mutane a jiharGyara
- Bulama Bukarti - Lauya mai kare haƙƙin ɗan Adam.
- Usman Albishir - (15 Yuni 1945 – 2 Yuli 2012) tsohon Sanata kuma shugaban marassa rinjaye a Majalisar Dattawa.
- Mai Mala Buni - (born 11 Nuwamba 1967) dan siyasa, tsohon sakataren jam'iyyar APC na kasa kuma Gwamnan jihar Yobe na yanzu.
- Ibrahim Gaidam, tsohon gwamnan jihar Yobe kuma a yanzu dan majalisar dattawa mai wakiltar shiyyar gabashin jihar a Majalisar Dattawa.
- Buba Galadima - Dan siyasa kuma sakataren kasa na tsohuwar jam'iyyar "Congress for Progressive Change (CPC)" .
- Bukar Ibrahim - (shekarar haihuwa Aktoba 1950) tsohon gwamnan jihar Yobe kuma tsohon dan takarar shugabacin kasa a jam'iyyar NNPP a shekarar 2007.
- Khadija Bukar Abba Ibrahim - (shekarar haihuwa 6 Janairu 1967) matar tsohon gwamnan jihar Yobe Bukar Abba Ibrahim, tsohuwar 'yar majalisar wakilai na tarayya kuma Ministar kasa mai kula da harkokin waje karkashin jagorancin Muhammadu Buhari
- Ahmed Ibrahim Lawan - Sanata tun daga shekarar 1991 kuma shugaban majilisar dattijan Najeriya a yanzu kuma shi ne mutum na 9 a shugabannin majalisar kasar.
- Ibrahim Talba - Dan siyasa kuma tsohon babban sakataren gwamnati a fadar shugaban kasa lokacin mulkin Olusegun Obasanjo kuma Ciroman masarautar Tikau
- Adamu Waziri - (shekarar haihuwa 14 Satumba 1952) dan siyasa kuma tsohon dan takarar gwamnan jihar Yobe a karkashin jam'iyyar PDP kana tsohon ministan 'yan sanda na kasa kuma tsohon ministan jami'an kula da lafiyar hanya
- Jamila Babayo - (shekarar haihuwa 17 Mayu, 1983) marubuciya ce da ta kasance mace ta farko a shiryar Arewa Maso Gabashin Najeriya da ta lashe gasar rubutu ta mata zallah ta BBC Hausa.
ManazartaGyara
Jihohin Najeriya |
Babban birnin tarayyar (Abuja) | Abiya | Adamawa | Akwa Ibom | Anambra | Bauchi | Bayelsa | Benue | Borno | Cross River | Delta | Ebonyi | Edo | Ekiti | Enugu | Gombe | Imo | Jigawa Kaduna | Kano | Katsina | Kebbi | Kogi | Kwara | Lagos | Nasarawa | Neja | Ogun | Ondo | Osun | Oyo | Plateau | Rivers | Sokoto | Taraba | Yobe | Zamfara |