Nnamdi Azikiwe, ɗan siyasar Nijeriya ne. An haife shi a shekara ta alif 1904 a garin Zungeru, dake Arewacin Najeriya; ya mutu a shekara ta alif 1996. Nnamdi Azikiwe shugaban kasar Najeriya neshi daga watan Oktoba 1963 zuwa watan Janairun 1966 (bayan Sarauniyar Ingila Elizabeth na biyu - kafin Johnson Aguiyi-Ironsi).

Nnamdi Azikiwe
1. shugaban ƙasar Najeriya

1 Oktoba 1963 - 16 ga Janairu, 1966
← no value - Johnson Aguiyi-Ironsi
Governor-General of Nigeria (en) Fassara

16 Nuwamba, 1960 - 1 Oktoba 1963
James Wilson Robertson (en) Fassara - no value →
Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya

1 ga Janairu, 1960 - 1 Oktoba 1960 - Dennis Osadebay (en) Fassara
Member of the Privy Council of the United Kingdom (en) Fassara

Rayuwa
Haihuwa Zungeru da Yankin Mulkin Mallaka na Arewacin Najeriya, 16 Nuwamba, 1904
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Harshen Ibo
Mutuwa Nsukka, 11 Mayu 1996
Ƴan uwa
Abokiyar zama Flora Azikiwe
Uche Azikiwe
Karatu
Makaranta Howard University (en) Fassara
Lincoln University (en) Fassara
University of Pennsylvania (en) Fassara
Columbia University (en) Fassara
Methodist Boys' High School (en) Fassara
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da marubuci
Kyaututtuka
Imani
Addini Kiristanci
Jam'iyar siyasa Majalisar Najeriya da Kamaru

Farkon Rayuwa gyara sashe

Nnamdi Azikiwe

An haifi Dr Nnamdi, Azikiwe a ranar 16 ga Nuwamba, 1904 a Zungeru, Jihar Neja, Najeriya. Azikiwe ya halarci makarantun firamare da sakandare daban-daban a garin Onitsha, Calabar , Lagos. Ya je kasar Amurka a 1925, inda ya halarci makarantu da yawa. Azikiwe ya sami takaddun shaida da digiri da yawa, gami da digiri na farko da na biyu daga Jami'ar Lincoln a Pennsylvania da digiri na biyu na biyu daga Jami'ar Pennsylvania. A 1934 ya tafi Gold Coast (yanzu Ghana), inda ya kafa jarida mai kishin kasa kuma ya kasance mai ba da shawara ga Kwame Nkrumah (wanda daga baya ya zama shugaban Ghana na farko) kafin ya dawo Najeriya a shekarar 1937.

Ya zama Sakatare-Janar na Majalisar Kasa Najeriya da Kamaru (NCNC). Bayan mutuwar Herbert Macaulay a Kano a shekarar 1946, ya zama shugaban NCNC. Ya samar da yankin Gabas tareda gabatar da gwamnatin yankin.[1].


An zabi Dr Azikiwe a matsayin Firimiya na yankin Gabas a 1954 karkashin Majalisar Kasa ta Najeriya (NCNC), sun yi takara a babban zaɓen 1959. Jam'iyyar sa tasamu mafi rinjayen kujeru a majalisar wakilai ta tarayya. Domin kafa gwamnati a matakin tarayya, jam’iyyar Dr Nnamdi Azikiwe (NCNC) ta kafa kawance da jam’iyyar[2] Arewa Peoples Congress (NPC). Daga baya aka nada shi a matsayin Gwamna-Janar na Najeriya a ranar 1 ga Oktoba, 1960. Da Nijeriya ta zama Jamhuriya a 1963, Dr Azikiwe ya zama shugaban Najeriya na farko. A jamhuriya ta biyu, Dr Nnamdi Azikiwe ya taka rawa sosai a zaben 1979. Ya yi takara a matsayin dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar NPP amma ya zo na uku a zaben.

Manazarta gyara sashe

Wannan Muƙalar guntuwa ce: tana buƙatar a inganta ta, kuna iya gyara ta.