Shuaibu Isa Lau

Dan siyasar Najeriya

Shuaibu Isa Lau (an haife shi a ranar 27 ga watan Nuwamban shekara ta 1960) sanata ne na Tarayyar Najeriya daga Jihar Taraba . Yana wakiltar Taraba ta Arewa a majalisar dokokin Najeriya ta tara. Sanata Lau shi ne kuma Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sayen Kayan Jama'a.

Shuaibu Isa Lau
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

5 ga Yuli, 2017 -
Abubakar Sani Danladi
District: Taraba North
Rayuwa
Haihuwa Lau (Nijeriya), 27 Nuwamba, 1955 (68 shekaru)
ƙasa Najeriya
Mazauni Abuja
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da ɗan kasuwa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Lau dan jam'iyyar PDP ne.

Yankin Sanatan Arewa, ya mamaye ƙananan hukumomi shida: ( Jalingo, Yorro, Zing, Lau, Ardo Kola da Karim Lamido ).

Yara da ilimi gyara sashe

An haifi Shuaibu Isa Lau a karamar hukumar Lau a cikin jihar Taraba ranar 27 ga watan Nuwamban shekara ta 1960 cikin dangin Alhaji Isa Ali da Hajiya Zainab Isa Ali. Ya fara karatunsa na ilimi a Makarantar Firamare ta Makarantar Lau, daga shekara ta 1969 zuwa shekarata 1975 sannan kuma Kwalejin Janar Murtala Muhammed, Yola don samun takardar shedar kammala karatun sakandare tsakanin shekara ta 1975 zuwa shekara ta 1980. Bayan haka, ya ci gaba zuwa Makarantar Nazarin Asali, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya a cikin shekara ta 1980, sannan daga baya ya koma bangaren Injiniya inda ya samu digiri na farko a kan Injiniya a shekara ta 1984.

Harkar siyasa gyara sashe

A shekara ta 2015, Lau ya shiga siyasa ta hanyar tsayawa takarar sanata na arewacin Taraba a karkashin inuwar jam'iyar People's Democratic Party amma Abubakar Danladi Sani ya yi kokarin neman kujerar kuma aka ayyana shi a matsayin wanda ya lashe. Daga baya ya nemi sasantawa a kotu kuma ya ci nasara a ranar 23 ga watan Yunin shekara ta 2017 don zama memba na majalisa ta 8 a Majalisar Dattawa har zuwa watan Yunin shekara ta 2019.

An sake zabarsa a karkashin jam’iyya daya, People Democratic Party a ranar 28 ga watan Maris na shekarata 2019 inda kuma ya samu kuri’u 113, 580 don kayar da babban abokin karawarsa, Ahmed Yusuf (Gamaliya) na All Progressive Congress wanda ya samu kuri’u 111,412 don wakiltar Taraba ta Arewa wani shekaru hudu. Shi ne Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sayen Kayan Jama'a a Majalisar Dokoki ta 9 ta majalisar dattijan Najeriya .

Rayuwar iyali gyara sashe

Sanata Lau ya auri Hajiya Fati Ibrahim Hassan Lau kuma ya albarkace ta da yara.

Manazarta gyara sashe