Amina Jane Mohammed[1] (an haife ta a ranar 27 ga watan Yunin shekara ta alif ɗari tara da sittin da ɗaya, 1961) ta kasance ƴar siyasan Najeriya da Birtaniya ce, wadda itace Mataimakiyar Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya. Gabanin ta riƙe Ministar Muhalli a tarayyar Najeriya tsakanin shekara ta dubu biyu da goma sha biyar, 2015 da shekarar dubu biyu da goma sha shida, 2016.[2]

Amina J. Mohammed
5. Deputy Secretary-General of the United Nations (en) Fassara

28 ga Faburairu, 2017 -
Jan Eliasson (en) Fassara
Minister of Environment (en) Fassara

11 Nuwamba, 2015 - 15 Disamba 2016
John Odey - Ibrahim Usman Jibril
Rayuwa
Haihuwa Jihar Gombe, 27 ga Yuni, 1961 (62 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta University of Reading (en) Fassara
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Employers Majalisar Ɗinkin Duniya
Columbia University (en) Fassara
Kyaututtuka
Mamba American Academy of Arts and Sciences (en) Fassara
Imani
Addini Musulunci

Kuruciya da Ilimi gyara sashe

An haifi Amina Jane Mohammed a Liverpool, dake England, a United Kingdom a ranar 27 ga watan Yunin shekara ta alif ɗari tara da sittin da ɗaya, 1961[3] ga iyaye likitan dabbobi da kuma mahaifiya mai kula da majinyata (nurse) 'yan asalin harshen Hausa-Fulani daga Najeriya.[4]

 
Amina J. Mohammed

Amina ta halarci makarantar firamare na Kaduna da birnin Maiduguri a Najeriya, sai kuma makarantar Makarantar "The Buchan School" da ke tsibirin Isle of Man.[5]Daga bisani ta halarci kwalejin Henley Management College a 1989.[6]Bayan ta kammala karatun ta ne mahaifinta ya nemi ta da ta dawo gida Najeriya.[7]

Ayyuka gyara sashe

A tsakanin shekarun, 1981 zuwa 1991, Amina tayi aiki da "Archcon Nigeria", wani kamfanin zane-zane da suke da alaka da kamfanin zane-zane na Norman and Dawbarn da ke United Kingdom.[8] A shekara ta, 1991 ta samar da kamfanin Afri-Projects Consortium, sannan daga shekara ta, 1991 zuwa 2001 itace darekta mai zartarwa na kamfanin.[9]

Daga shekara ta, 2002 har zuwa shekara ta, 2005, Amina ta shirya wani gangami da ilimantarwa game da jinsi karkashin United Nations Millennium Project.[10]

Amina ta rike matsayin mataimakiya na musamman ( Senior Special Assistant) na shugaban kasa akan shirin Millennium Development Goals (MDGs). A cikin shekara ta, 2005, an zarge ta da amfani da kudin tallafi na kasa a wajen ayyukan MDGs.

Amina ta kasance wacce ta kafa kuma ta samar da kamfanin Center for Development Policy Solution, sannan kuma a matsayin farfesa na daliban masters a jami'ar Columbia. A tsakanin wannan lokaci, tayi aiki a matsayin mai bada shawarwari na kungiyoyi daban daban na duniya wanda ya hada da, babban sakatariya a Majalisar Dinkin Duniya (UN) don zama na musamman akan Post-a shekara ta, 2015 "Development Agenda"; da kuma Independent Expert Advisory Group.

Sannan har wayau ta rike matsayin chairman na majalisin United Nations Educational, Scientific and Cultural Organization (UNESCO), sashin bincike da bayanai akan ilimi na duniya "Global Monitoring Report on Education" (GME).[11]

 
Amina J. Mohammed

Har zuwa shekara ta, 2012, Amina tana daya daga cikin muhimman mutane a taron e Post-a shekara ta, 2015 Development Agenda, inda take aiki a matsayin mai bada shawara na musamman ga shugaban majalisar dinkin duniya watau Ban Ki-moon,[12][13] sannan tana daga cikin mutane na musamman na "High Level Panel of Eminent Persons (HLP)" da majalisar Open Working Group (OWG) da dai sauransu.[14] Daga shekara ta, 2014, tayi aiki a matsayin babban sakatariya na "ndependent Expert Advisory Group on the Data Revolution for Sustainable Development".[15]

Ministan Muhalli (2015-2017) gyara sashe

Amina tayi aiki a matsayin ministan muhalli a karkashin mulkin shugaba MUhammadu Buhari daga watan Nuwamaban shekara ta, 2015 zuwa watan Febrerun shekara ta, 2017.[16] A wannan lokaci itace wakiliyar Najeriya a Kungiyar Kasashen Nahiyar Afurka wato "African Union (AU)" fannin jawo canji wanda Paul Kagame ke jagoranta.[17] Ta ajiye aiki da kungiyar Nigerian Federal Executive Council a ranar 24 ga watan Febrerun shekara ta, 2017.[18]

 
Amina J. Mohammed

A cikin shekara ta, 2017, wata kungiya mai zaman kanta ta zargi Amina da cewa tana ba da izini ga kamfanonin kasar China wajen diban itace timber zuwa kasashensu ba tare da izinin gwamnatin tarayya ba, a lokacin tana ministan muhalli na Najeriya.[19][20][21]Amma daga bisani gwamnatin Najeriya ta karyata zargin.[22]

Sauran Ayyuka gyara sashe

Martabawa gyara sashe

Rayu gyara sashe

Aure

Manazarta gyara sashe

  1. "UN Framework Convention on Climate Change - Participants" (PDF). United Nations. 2 May 2017. Retrieved 30 September 2018.
  2. Oak TV. "Amina J. Mohammed resumes at the Federal Ministry of Environment as Minister". oak.tv. Archived from the original on 14 April 2019. Retrieved 27 February 2017.
  3. "Sustainable Development Solutions Network | Amina Mohammed". unsdsn.org. Archived from the original on 15 December 2016. Retrieved 8 December 2016.
  4. "Mark Seddon (May 26, 2017). "'Why is she here?': the Nigerian herder's daughter who became UN deputy chief". The Guardian. United Kingdom. Retrieved October 18, 2017.
  5. "Hester Lacey (December 7, 2017), Amina J Mohammed on Nigeria, leadership and the UNFinancial Times.
  6. "Federal Ministry of Environment Archived2019-10-30 at the Wayback Machine Federal Government of Nigeria.
  7. "Mark Seddon (May 26, 2017). "'Why is she here?': the Nigerian herder's daughter who became UN deputy chief". The Guardian. United Kingdom. Retrieved October 18, 2017.
  8. "Nigeria: MDGs and Amina Az-Zubair's Footprint 24-November-2011". Allafrica.com. 2011-11-24.
  9. Secretary-General Appoints Amina J. Mohammed of Nigeria as Special Adviser on Post-2015 Development Planning United Nations, press release of June 7, 2012.
  10. Secretary-General Appoints Amina J. Mohammed of Nigeria as Special Adviser on Post-2015 Development Planning United Nations, press release of June 7, 2012.
  11. Secretary-General Appoints Amina J. Mohammed of Nigeria as Special Adviser on Post-2015 Development Planning United Nations, press release of June 7, 2012.
  12. Secretary-General Appoints Amina J. Mohammed of Nigeria as Special Adviser on Post-2015 Development Planning United Nations, press release of June 7, 2012.
  13. Kaye Wiggins (June 2, 2015), UN sets sights on sustainable development goals Financial Times.
  14. ProsperCSIS (23 July 2014). "Amina Mohammed, Special Adviser to the UN Secretary-General on Post-2015 Development Planning"
  15. Independent Expert Advisory Group MembersThe UN Secretary General's Independent Expert Advisory Group on a Data Revolution for Sustainable Development.
  16. Amina J. Mohammed, Deputy Secretary-GeneralUnited Nations.
  17. AU Reforms Advisory Committee African Union.
  18. "Oak Tv. "Amina J. Mohammed's emotional speech as she steps down as Nigeria's Environment Minister". oak.tv. Oak TV. Retrieved 27 February 2017.
  19. "U.N.'s No. 2, Amina Mohammad, accused in Chinese scam". Japan Times. November 10, 2017.
  20. "UN's number two accused in Chinese scam to import Nigerian rosewood". November 9, 2017.
  21. "New Allegations Challenge the Environment Record of Top U.N. Official". November 9, 2017.
  22. "Rosewood Export: UN's Amina Mohammed did no wrong, Nigerian govt says". November 12, 2017.
  23. High-Level Group of Personalities on Africa-Europe Relations Archived 2022-04-11 at the Wayback Machine Africa Europe Foundation (AEF).
  24. Board of Directors Global Partnership for Sustainable Development Data.
  25. Members International Gender Champions (IGC).
  26. Leadership World Economic Forum's Young Global Leaders.
  27. Amina Mohammed to Receive Ford Family Notre Dame Award University of Notre Dame, press release of November 4, 2015.
  28. Shelbie Bostedt (November 13, 2017), Diplomat of the Year Honoree Amina J. Mohammed Discusses Future of United Nations Foreign Policy.
  29. Waweru, Nduta (8 July 2018). "Deputy Secretary-General of the U.N. Amina J. Mohammed crowned Queen in Niger". Face2FaceAfrica. Retrieved 19 October 2019.
  30. "BBC 100 Women 2018: Who is on the list?" (in Turanci). 2018-11-19. Retrieved 2019-04-20.
  31. "Meet the Winner of the 2019 Global Citizen World Leader Prize".
Wannan Muƙalar guntuwa ce: tana buƙatar a inganta ta, kuna iya gyara ta.