Col (mai ritaya) Abdulmumini Aminu (an haife shi a shekara ta 1949) ya kasance gwamnan mulkin soja a Jihar Borno, Nijeriya tsakanin watan Agustan shekara ta 1985 da Disamba shekara ta 1987 a lokacin mulkin Janar Ibrahim Babangida a Najeriya.[1]

Abdulmumini Aminu
Gwamnan Jihar Borno

ga Augusta, 1985 - Disamba 1987
Abubakar Waziri - Abdul One Mohammed (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Katsina, 1949 (74/75 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Daga baya ya zama Shugaban ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya, sannan ya zama Shugaban ƙungiyar Ƙ'ƙwallon ƙafa ta Yammacin Afirka.

Aikin soji gyara sashe

Aminu yana ɗaya daga cikin hafsoshin da suka kame Janar Muhammadu Buhari a juyin mulkin watan Agustan shekara ta 1985 inda Janar Ibrahim Babangida ya hau ƙaragar mulki.[2]

Har wayau Aminu ya kasance Manjo a cikin shekaru talatin lokacin da Babangida ya naɗa shi gwamnan jihar Borno a ƙarshen wannan watan.[3]

A taron farko da aka yi a Najeriya game da cutar kanjamau a watan Oktoba na shekara ta 1987, Aminu ya ce cewa cutar kanjamau ta samo asali ne daga Afirka dangane da duk neman wariyar launin fata, saboda wani tunani da ke dangane da duk wani abin da ke mara kyau da ga abin da ake kira nahiya mai duhu.[4]

A matsayinsa na Gwamnan Borno, Aminu ya fuskanci ƙalubale saboda rashin kuɗi, kuma da farko ya bijirewa hukumarsa a matsayin bako. Ya ba ilimi fifiko, fiye da duk wani abu dumin kasancewar sa na mai mulki don sauke haƙƙin dake kansa.[5]

Bayan wa’adin sa na gwamna, Aminu ya zama malami a Kwalejin Sojoji da Kwalejin Ma’aikata, Jaji. Sannan an nada shi mataimakin sakataren soja, sannan Brigade Commander sannan kuma mai rikon mukamin Janar Kwamanda Jos . Sannan an naɗa shi Kwamandan Tsaro na Kasa, wanda ke da alhakin inganta tsaron kasa. Aminu yayi ritaya lokacin da Janar Sani Abacha ya hau mulki.[5]

Ƙwallon ƙafa gyara sashe

Aminu ya kasance Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFA) a shekara ta 1997.[6]

A gasar cin Kofin Duniya ta Faransa '98, ya ba da umarnin biyan dala dubu 8 ga kowannensu ga 'yan wasan Najeriya, duk da rashin nasarar da suka yi a hannun Paraguay a wasan rukuni na karshe na gasar. A watan Afrilun a shekara ta 1999, yayin da Shugaban NFA Aminu ya kasance shugaban Kwamitin Shirye-shiryen Cikin Gida na Najeriya, yana shirin karbar bakoncin ’yan wasan kwallon Kofin Duniya a Filin Wasannin Liberty, Ibadan a lokacin gasar FIFA ta Matasan Duniya a shekarata 1999 .

A watan Yulin shekara ta 2004, Aminu ya kasance mataimakin shugaban kwamitin mutum 17 da aka kafa don sake shirya Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya.[7]

Ya kasance cikin gasa tare da Air Commodore Emeka Omeruah don a zaba a matsayin shugaban kungiyar kwallon kafa ta Afirka ta Yamma (WAFU) a cikin shekara ta1999. A watan Nuwamban shekara ta 1998, gwamnati ta nuna goyon bayan sa ga Omeruah.[8]

A watan Maris a shekara ta 1999, shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Ghana ya ba da goyon bayansa ga neman Aminu, in har ya nuna sha’awar aikin.[9]

Aminu ya zama shugaban ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Afirka ta Yamma daga shekarar 1999 zuwa 2002, kuma memba a Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka.[5][10]

Ya sanya burin sa don sake karfafa ƙungiyar da ta kusan mutuwa.[11]

Siyasa gyara sashe

Aminu ya koma Jam’iyyar PDP ne a farkon Jamhuriya ta Hudu ta Najeriya . Daga baya ya sauya sheka zuwa jam'iyyar (United Nigeria People Party (UNPP).[12] Aminu ya tsaya takarar gwamnan jihar Katsina a watan Afrilun shekara ta 2003, amma bai samu nasara ba a kan mai ci yanzu Umaru Musa Yar'adua, wanda daga baya ya zama Shugaban Najeriya.[13]

A watan Afrilun shekara ta 2004, Aminu ya koma PDP, yana mai cewa UNPP ta rikice.[12] A watan Yunin shekara ta 2007, Aminu ya shiga takarar neman maye gurbin Bala Bawa Ka'oje a matsayin Shugaban Hukumar Wasannin Kasa.[14] Aikin gaskiya an ba Abdulrahman Hassan Gimba.[15]

Manazarta gyara sashe

  1. "Nigeria States". WorldStatesmen. Archived from the original on 28 May 2010. Retrieved 2010-05-12.
  2. Simon Kolawole (24 May 2009). "Leadership Without Conscience". ThisDay. Retrieved 2010-05-12.
  3. Sunday Isuwa (25 April 2010). "Melaye Under Fire Over Comment On IBB". Archived from the original on 13 July 2011. Retrieved 2010-05-12.
  4. JAMES BROOKE (November 19, 1987). "In Cradle of AIDS Theory, a Defensive Africa Sees a Disguise for Racism". The New York Times. Retrieved 2010-05-12.
  5. 5.0 5.1 5.2 Ibrahim Modibbo (21 September 2008). "'The Yar'Adua I Know, Will Make History'". Leadership. Retrieved 2010-05-12.
  6. "Cesare Maldini has no complaints..." Agence France Presse. December 6, 1997. Archived from the original on August 15, 2003. Retrieved 2010-05-12.
  7. Juliana Taiwo (9 July 2004). "Babayo Shehu Heads NFA Restructuring C'ttee". ThisDay. Retrieved 2010-05-12.
  8. Dan Okereke (25 November 1998). "Omeruah Floors Aminu". P.M. News. Retrieved 2010-05-12.
  9. Opeyemi Omotayo (9 March 1999). "Ghana Supports Aminu's Bid". P.M. News (Lagos). Retrieved 2010-05-12.
  10. "History". West Africa Football Union. Archived from the original on 2011-04-05. Retrieved 2010-05-12.
  11. "Aminu Holds Talks With Eyadema". P.M. News. 6 December 1999. Retrieved 2010-05-12.
  12. 12.0 12.1 "Ex-Governor Rejoins PDP". ThisDay. 2 April 2004. Retrieved 2010-05-12.
  13. Jare Ilelaboye (April 21, 2003). "Yar'adua Retains Seat in Katsina". This Day. Retrieved 2010-05-12.
  14. Olawale Ajimotokan (12 June 2007). "Aminu in Race for NSC Top Job". ThisDay. Retrieved 2010-05-12.
  15. "Yar'Adua names cabinet". Africa News. 27 July 2007. Archived from the original on 28 September 2011. Retrieved 2009-12-15.