Rikicin Jos, 2008

Tarzoma mai nasaba da addini a Najeriya

Rikicin Jos na shekara ta 2008 ya kasance tarzoma ce da ta shafi kiristoci da musulmi dangane da sakamakon zaben kananan hukumomi da aka gudanar a ranakun 28 da 29 ga watan Nuwamba 2008 a garin Jos dake yankin Middle Belt a Najeriya.[1][2] Rikicin na kwanaki biyu ya yi sanadin jikkata ɗaruruwa, yayin da aƙalla mutane 761 suka mutu.[3] An tura sojojin Najeriya (a yankin).[4]

Infotaula d'esdevenimentRikicin Jos, 2008
Iri riot (en) Fassara
Kwanan watan 29 Nuwamba, 2008
28 Nuwamba, 2008
Ƙasa Najeriya
Participant (en) Fassara
Adadin waɗanda suka rasu 761
Wurin Jos a Najeriya

Dalilai gyara sashe

Ma’aikatan zaɓe dai ba su fito fili sun bayyana sunayen waɗanda suka yi nasara a zaɓen ba, sai aka fara yada jita-jitar cewa ɗan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Barista Timothy Gyang Buba ne ya lashe zaɓen,[5] ya doke ɗan takarar jam’iyyar All Nigerian Peoples Party. Jama’ar al’ummar Hausawa Musulmi, sun fara gudanar da zanga-zanga tun kafin a fitar da sakamakon, wanda ya haifar da arangama da ta yi sanadiyar mutuwar daruruwan mutane tsakanin Musulmi da Kirista, wadanda suka fi goyon bayan Buba.[6]

Wai-wa-ye gyara sashe

Irin wannan tarzoma da aka yi a shekarar 2001 tsakanin Kirista da Musulmi a Jos ma ta yi sanadiyyar mutuwar ɗaruruwan mutane.[7] Rikicin 2004 a Yelwa, wani gari a Jihar Filato ya haifar da abin da ake kira Kisan Yelwa. Fadan da aka yi a jihar Kaduna ta arewa ta tsakiya a lokacin da aka yi yunƙurin kafa shari’ar Musulunci a shekarar 2000, ya haifar da raba garin Kaduna. Hakan ya biyo bayan tarzomar Kaduna a watan Nuwamban shekarar 2002, sakamakon yadda Najeriya ta karbi bakuncin gasar Miss World, wadda daya daga cikin wadanda suka fafata ta lashe gasar a bara.[8]

Tarzomar gyara sashe

Rikicin na kwanaki biyu ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 761,[3] sai kuma gidaje, masallatai, coci-coci da makarantu sun lalace ko an kona su.[9][10] Ƙungiyar agaji ta Red Cross ta Najeriya ta bayar da rahoton cewa mutane 10,000 ne suka tsere daga gidajensu saboda tarzomar,[2][11] kuma suna zaune a matsugunan da gwamnati ta samar na wucin gadi.[6] An tura sojojin Najeriya cikin birnin domin magance rikicin, gami da shiga a tsakanin Kiristoci da Musulmai.[12] An soke tashin jirage izuwa Jos, an kuma toshe hanyoyin arewa.[13]

Tasiri gyara sashe

Jonah Jang, gwamnan jihar Filato, ya sanya dokar hana fita ta sa'o'i 24 a gundumomi hudu na birnin, kuma an ba sojoji damar "harbi" don hana sake afkuwar tashin wata tarzomar.[6] hukumar Human Rights Watch ta yi zargin cewa sojoji da ƴan sanda sun yi kisan gilla fiye da 130 a lokacin da suke mayar da martani kan tarzomar.[9] An kama matasa da yawa ɗauke da makamai na dukkan bangarorin biyu-(musulmai da kiristoci) a shingayen titin sojoji.[12] Ƴan sanda sun ce an kama sama da mutane 500 sakamakon tarzomar. Sai dai jami'an jihar sun ce babu wanda aka samu nasarar gurfanar da shi a gaban kuliya.[3]

Duba kuma gyara sashe

Manazarta gyara sashe

  1. "7,070 displaced persons in 10 camps in Jos, Nigeria". Xinhua News Agency. 6 December 2008. Archived from the original on 10 December 2008. Retrieved 5 December 2008.
  2. 2.0 2.1 "Riots 'kill hundreds in Nigeria'". BBC News. 29 November 2008. Archived from the original on 30 November 2008. Retrieved 30 November 2008.
  3. 3.0 3.1 3.2 Human Rights Watch (12 December 2013). "Leave Everything to God": Accountability for Inter-Communal Violence in Plateau and Kaduna States, Nigeria. pp. 45–47. Archived from the original on 21 April 2015. Retrieved 5 May 2015.
  4. Abubakar, Aminu. "Nigerian army takes over riot city". Agence France-Presse. Retrieved 5 May 2015.
  5. "Nigeria: Dozens Killed in Jos LG Election Riot". Allafrica.com. 29 November 2008. Archived from the original on 2 December 2008. Retrieved 30 November 2008.
  6. 6.0 6.1 6.2 "At Least 200 Die in Nigeria Clashes". The New York Times. 29 November 2008. Retrieved 30 November 2008.
  7. "Nigerian president tours riot city". BBC. 17 October 2001. Archived from the original on 4 December 2008. Retrieved 30 November 2008.
  8. "Nigeria calls off Miss World show". BBC. 23 November 2002. Retrieved 5 May 2015.
  9. 9.0 9.1 Human Rights Watch (20 July 2009). Arbitrary Killings by Security Forces: Submission to the Investigative Bodies on the November 28-29, 2008 Violence in Jos, Plateau State, Nigeria. Retrieved 5 May 2015.
  10. "300 bodies taken to mosque on 2nd day of Nigeria riots". CNN. 29 November 2008. Archived from the original on 3 February 2023. Retrieved 30 November 2008.
  11. "Nigerian army takes over city hit by Muslim-Christian clashes". The Telegraph. 30 November 2008. Retrieved 13 July 2015.
  12. 12.0 12.1 "At least 200 killed in clashes in Nigeria". Reuters. 29 November 2008. Archived from the original on 4 December 2008. Retrieved 30 November 2008.
  13. Rice, Xan (30 November 2008). "Nigerian city counts its dead after days of Christian-Muslim riots". The Guardian. Retrieved 5 May 2015.

Hanyoyin haɗi na waje gyara sashe