Nkeiruka Onyejeocha

Ƴar siyasar Najeriya

Nkeiruka Chidubem Onyejocha (an haife ta a ranar 23 Nuwamba shekarar 1969) yar siyasan Nijeriya ce kuma babban mai zartarwa a Majalisar Wakilan Tarayyar Najeriya.[1] Tana wakiltar Mazabar Tarayyar Isuikwuato / Umunneochi ta jihar Abia.[2]Onyejocha memba ce mai aiki a majalisar tarayyar Najeriya kuma galibi tana bayar da gudummawa sosai ga muhawarori da suka shafi mahimman batutuwan ƙasa a majalisa. Ta dauki nauyin tsare-tsare da dama tare da kawo yunkuri wadanda suka inganta rayuwar talakawan kasa da kuma taimakawa wajen kare hakkinsu.[3]

Nkeiruka Onyejeocha
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

11 ga Yuni, 2019 -
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

9 ga Yuni, 2015 - 9 ga Yuni, 2019
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

ga Yuni, 2011 -
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

5 ga Yuni, 2007 - 6 ga Yuni, 2011
District: Umunneochi (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Umu Nneochi da Umunneochi (en) Fassara, 23 Nuwamba, 1969 (54 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Harshen Ibo
Karatu
Makaranta Jami'ar Najeriya, Nsukka
Harsuna Turanci
Harshen Ibo
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party
All Progressives Congress

A cikin shekarar 2017 ta dauki nauyin wani kudiri wanda ya sanya jinyar gaggawa ga wadanda aka harba da bindiga ya zama tilas ga asibitoci ba tare da neman ko jinkirta jinya wai don jiran bayanai daga ‘yan sanda kafin a fara magani a yanayin gaggawa.

An fara zaben Onyejocha ne a shekara ta 2007 a karkashin jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP jam'iyya mai mulki na lokacin. Ta sauya sheka zuwa jam'iyyar All Progressive Congress, APC a shekarar 2018 bayan ta fuskanci matsin lamba daga tsaffin shugabannin jam’iyyar don ta dakatar da kudirin ta na komawa majalisa.[4] A shekarar 2019, ta sake lashe zaben fidda gwani na karo na hudu a Majalisar dokoki na Najeriya. Tana daya daga cikin mafiya dadewa a majalisa.[5][6][7]

A cikin shekara ta 2019, Onyejocha ta tsaya takarar matsayin Speaker na Majalisa Wakilai a kasa da maza suka mamaye mukamai, tare da abokin adawa Femi Gbajabiamila daga Jihar Legas wanda ƙungiya - jama'iyyar adawa ta APC, APC ta tsaida. Babban matasalar zaben Onyejocha shi ne ta kasance a matsayin mai magana da yawun shiyyar ta na yankin kudu maso gabashin Najeriya domin daidaita manyan ikon tarayya a tsakanin shiyyoyin siyasa shida na kasar. Amma ta ajiye takarar tsakanin awanni 24 zuwa zaben.

Onyejocha ya kasance Shugaban rikon kwarya na Karamar Hukumar Umunneochi ta Jihar Abia a shekarar 2002. A shekara ta 2003 tayi aiki a majalisar zartarwa ta jihar Abia a matsayin kwamishina kan kula da albarkatu da cigaban ma'aikata.

Rayuwar farko, ilimi da aiki gyara sashe

Onyejocha diya ce ga Eze Bob Ogbonna ne a garin Isuochi na karamar hukumar Umunneochi ta jihar Abia. Ta rasa mahaifiyarta tun tana karama. Onyejocha ta halarci Makarantar Firamare ta Isuochi Central da kuma Ovim Girls School, Isuochi. A cikin shekara ta 1988 ta kammala karatun digiri daga jami'ar Najeriya, Nnsuka, UNN tare da difloma a fannin Social Work/Community Development. A shekarar 1993 ta kammala karatun digiri na farko a fannin Bachelor of Art tare da sakamakon second class upper (a Daraja) daga Jami'ar Najeriya, Nsukka. Onyejocha ta yi Digiri na biyu a kan Harkokin Kasa da Kasa da diflomasiyya (International Affairs and Diplomacy) daga Jami’ar Jihar Imo a shekarar (2005) da kuma Digiri na Biyu a hada-hadan jiragen ruwa daga Jami’ar Fasaha ta Ladoke Akintola University of Technology, Jihar Oyo.

A lokacin da take karatun ta na digiri a jami'a, Onyejocha ta kasance mai himma a harkokin dalibai da siyasa. Ta rike mukamai daban-daban na shugabanci a gwamnatin kungiyar dalibai ta jami’ar Najeriya, Nnsuka, UNN. Onyejocha ta yi aiki a ofishin ladabtarwa na gwamnan jihar Osun a yayin da take hidimar bautar kasa na shekara daya a shekarar 1993. An ce ra'ayinta na siyasa ya samo asali ne daga nan.

Ta kasance Manajan Darakta na Nikkings da Kingzol International Ltd da ke kula da jarirai da kayayyakin gida. An yaba wa shugabancin ta saboda daga darajar kamfanin zuwa matakin kasuwanci na kasa da kasa. Kamfanin mallakin mijinta ne, Sir Kingsley Onyejocha.[8][9][10]

Harkar siyasa gyara sashe

Shugaban Karamar Hukuma kuma Kwamishina gyara sashe

Siyasar Onyejocha ta fara ne da nadin ta a shekarar 2002 zuwa majalisar zartarwa ta jihar Abia a matsayin kwamishina na da Gudanar da Albarkatun Kasa da Bunkasa ayyukan jama'a wato (Resource Management and Manpower Development) na Gwamna Orji Uzor Kalu. Ana tuna ta da kafa cibiyoyin koyon ayyukan hannu a duk faɗin jihar Abia. A shekarar 2003 ta kasance Shugabar rikon kwarya na karamar hukumar Umunneochi ta jihar Abia. A lokacin da take kan karagar mulki, ta aiwatar da ayyukan shawo kan zaizayar kasa, da inganta tsaro a tsakanin al'umma, da aiwatar da gyaran hanyoyi. Saboda jin dadin aikinta, Majalisar Sarakunan Gargajiya Umunneochi ta ba ta sarauta ta Adaejiagamba- (yar jakadiya). Ita ce ta fara karbar wannan taken.[11]

Zabe a majalisar wakilan tarayyar Najeriya gyara sashe

An fara zaben Onyejocha a majalisar wakilai ta tarayyar Najeriya a 2007 a karkashin jam'iyyar PDP. Manufofin ta na siyasa sun mai da hankali kan samar da dokoki don bunkasa rayuwar mata da yara; matasa da masu karamin karfi; inganta ilimi, kiwon lafiya da samar da kayan more rayuwa .

A yayin taron majalisar karo na bakwai an ba ta mace mafi kwazo a majalisar dokoki a Najeriya daga Kungiyar Ma’aikatan Majalissar Dokokin Najeriya (PASSAN). Onyejocha ita ce shugabar mata ta farko a kwamitin majalisar wanda aka kirkiro yayin taro na shida tsakanin 2007 da 2011. Ta jagoranci mata ‘yan majalisu a kokarin shawo kan matsalar rashin daidaito tsakanin maza da mata da inganta yanayin rayuwar yara da kuma marasa karfi.

A shekarar 2011 an nada ta shugaban kwamiti na harkokin jiragen sama wanda a lokacin ana fama da al'amuran tsaro. Ayyukan ta na hangen nesa sun haifar da inganta filayen jiragen saman Najeriya zuwa matakin filayen jiragen sama na duniya. Aikin ta a Kwamitin na harkokin jiragen sama ya kasance mara cikas kuma mai tasiri wanda hakan ya zama abin ishara ga sauran kwamitocin na majalisa. A cikin shekara ta 2013 ne ta yi kira don cikakken bincike da kuma gurfanar da jami'an, wanda duk yake da hannu a wajen kawo tasgwaro ga lafiyar jirgin sama ya wanda ya jawo hadarin jirgi dauke da fasinjoji wato Dana Air Flight 992 a kan hanya daga babban birnin Najeriya Abuja zuwa Lagos a ranar 3 Yuni 2012. Dukkanin mutane 153 da ke cikin jirgin da kuma mutane 6 da ke kasa sun mutu.[12][13][14][15]

A shekarar 2013 Onyejocha ta sanya fifikon kasa a kan son zuciya yayin da ta yi kira da a bincike akan Stella Oduah, ministar jirgin sama wacce ta fada cikin zargin rashawa bayan da aka ruwaito ta sayi motoci biyu BMW da darajarsu ta kai naira miliyan 250 ga ma'aikatar jirgin sama ba tare da amincewa ba. Onyejocha ya sha suka a bainar jama'a daga dangin ta saboda a fili ta nemi a binciki Stella Oduah.

Financialarfin ikon ƙananan hukumomi gyara sashe

Tsarin mulkin Jamhuriyar Tarayyar Najeriya, (Canji na Hudu) Dokar, Mai lamba 5, 2017 (Rarraba Ruwan Baza): Dukkanin majalisun dokokin kasar sun amince da kudirin amma yana jiran amincewar majalisun dokokin jihohi.

Manazarta gyara sashe

  1. "Hon. Nkeiruka Onyejeocha – The Abia State Government – Official Website". www.abiastate.gov.ng. Retrieved 2019-11-25.
  2. http://www.abiastate.gov.ng/abia-personalities/2814/ Archived 2019-07-02 at the Wayback Machine
  3. "Female presidency possible in 2023 -Senator Onyejeocha". Punch Newspapers. 2021-09-19. Retrieved 2022-02-21.
  4. "PHOTO: Hon. Nkiruka Onyejeocha dumps PDP for APC". Yellow Danfo. August 25, 2018. Retrieved November 20, 2019.
  5. "National Assembly | Federal Republic of Nigeria". www.nassnig.org. Retrieved 2019-11-25.
  6. "Hon. Nkeiruka Onyejeocha biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2019-11-25.
  7. "Onyejeocha: Amazon on firing line - The Nation Nigeria". The Nation Nigeria. 2017-03-01. Retrieved 2017-03-28.
  8. "Profile in Leadership: Hon. Onyejocha Onyejeocha". Weekenders Magazine. September 19, 2012. Retrieved November 20, 2019.
  9. "Hon. Onyejeocha Nkeiruka". Retrieved 2019-11-25.
  10. "Onyejeocha Chidubem :: Shine your eye". www.shineyoureye.org. Retrieved 2019-11-25.
  11. "Onyejeocha: A heart for service". The Nation Newspaper. 2017-02-24. Retrieved 2019-11-27.
  12. "153 passengers dead in Dana Air crash in Lagos - Premium Times Nigeria". 2012-06-03. Retrieved 2019-11-27.
  13. "Nsehe, Mfonobong. "Plane Crash In Nigeria Kills 152 Passengers". Forbes. Retrieved 2019-11-27.
  14. "Laing, Aislinn (2012-06-04). "Bodies recovered from passenger plane crash site in Lagos". ISSN 0307-1235. Retrieved 2019-11-27.
  15. "Olawoyin, Oladeinde (2017-03-14). "Why Dana plane crashed in 2012 – Final Investigation Report - Premium Times Nigeria". Retrieved 2019-11-27.

Hanyoyin haɗin waje gyara sashe


</br>Kudirin Gyara Kundin Tsarin Mulki da 8th ya Amince da shi Archived 2020-11-29 at the Wayback Machine