Clarence Olafemi ‘yar siyasar Najeriya ce da aka nada a karkashin mukaddashin gwamnan jihar Kogi a watan Fabrairu shekara ta 2008, bayan da aka soke zaben gwamna Ibrahim Idris . Ya mika wa Ibrahim Idris a ranar 29 ga watan Maris shekara ta 2008 bayan Idris ya sake lashe zabe [1].

Clarence Olafemi
Gwamnan jahar kogi

6 ga Faburairu, 2008 - 29 ga Maris, 2008
Ibrahim Idris - Ibrahim Idris
Rayuwa
Haihuwa Mopa-Muro
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Yarbanci
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Turanci
Yarbanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

An haifi Olafemi a karamar hukumar Mopa-Muro ta jihar Kogi. Ya kammala karatunsa a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria . Ya kasance dan takarar gwamna na jihar Kwara .

An zabi Olafemi a matsayin dan majalisar dokokin Jihar Kogi mai wakiltar mazabar Mopamuro a watan Afrilu shekara ta 2007 akan dandalin jam'iyyar People's Democratic Party (PDP). A watan Satumban shekara ta 2007, kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Kogi da ke Lokoja ta soke zabensa. Ya daukaka kara kan hukuncin, kuma a watan Fabrairu shekara ta 2008, Kotun daukaka kara da ke Abuja ta soke hukuncin. A watan Yulin 2008, an kira shi a gaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) domin ya bayyana rawar da ya taka wajen karkatar da naira biliyan 12 na jihar .

Manazarta gyara sashe

  1. Kunle Olasanmi (7 February 2008). "Kogi Speaker takes over as Idris loses appeal". The Nation. Archived from the original on 2009-05-10. Retrieved 2009-12-13.