Alhaji Dr. Aliyu Akilu MFR An haife shi a shekara ta alif 1918, ya rasu 19 ga watan oktoban shekara ta alif 1999 wanda kuma aka sani da Malam Akilu Aliyu ko Aqilu Aliyu ɗan Najeriya ne mawãƙi, marubuci, masanin ilimi, ɗan siyasa, kuma daya daga cikin manyan marubuta waƙoƙin Hausa a karni na ashirin.

Aliyu Akilu
Rayuwa
Haihuwa 1918
ƙasa Najeriya
Mutuwa 1998
Karatu
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a maiwaƙe

Tarihin Rayuwa gyara sashe

An haifi Akliu Aliyu a garin Jega (a wani ƙauye da ake kira Kyarmi, a cikin jihar Kebbi ta yanzu). Malam Akilu ya yi mafi yawan rayuwarsa a jihar Kano Kano, wurin da ya je a matsayin dalibin Islamiyya tun yana saurayi. Ya kasance a Maiduguri na 'yan shekarun da suka gabata kafin ya dawo Kano inda ya zauna har zuwa rasuwarsa. Ya rayu a matsayin malamin Islama, tela kuma mawaƙi (waƙa ta kasance hanya da ya koyar da dubban ɗalibai marasa adadi). Ya kafa, kuma ya koyar a, makarantun Islamiyya a Maiduguri da Azare.

Harkar Ilimi gyara sashe

Dangane da karatunsa da farko dai ya fara samun horo a makarantar Al-Qur'ani a Kano, karkashin malaman Tijjaniyya, sannan kuma daga baya ya tafi Borno yin karatu a gaban manya-manyan malaman addinin Islama daga yankin arewa maso gabashin kasar. Ya kasance mawaki mai kaifin basira kuma yana rubutun waƙoƙin sa ne cikin harsunan Hausa da Larabci, kuma waƙen nasa ya samu karbuwa sosai a tsakanin yawancin masu jin Hausa. Ya fara rubuta wakokin Larabci a cikin shekarun 1930.

Ayyuka gyara sashe

Mashahuran Wakoki Sun Hada da gyara sashe

  • Matan Aure
  • Dan Gata
  • 'Yar Gagara
  • Hausa Mai Ban Haushi
  • Maza mamugunta
  • Wakar Najeriya
  • Cuta ba mutuwa ba

Manazarta gyara sashe