Abubakar Atiku Bagudu
Abubakar Atiku Bagudu (An haife shi a ranar 26 ga watan Disamba shekara ta alif 1961) Dan Najeriya ne, kuma dan siyasa, wanda ya taba zama Sanatan Jihar Kebbi ta tsakiya, kuma ya rike mukamin Ministan Babban Birnin Tarayya a watan December 2008. ya zama dan takarar gwamna a karkashin jam'iyar All Progressives Congress (APC) a zaben shekarar 2015 kuma ya samu nasarar zama Gwamna da sau biyu 2015-2019 da kuma 2019-2023.[1]
Abubakar Atiku Bagudu | |||||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|
29 Mayu 2015 - 29 Mayu 2023 ← Aminu Musa Habib Jega (en)
6 ga Yuni, 2011 - 4 ga Yuni, 2015 District: Kebbi Central
5 ga Yuni, 2007 - District: Kebbi Central
2003 - 2007 | |||||||||
Rayuwa | |||||||||
Cikakken suna | Abubakar Atiku Bagudu | ||||||||
Haihuwa | Gwandu, 26 Disamba 1961 (62 shekaru) | ||||||||
ƙasa | Najeriya | ||||||||
Harshen uwa | Hausa | ||||||||
Karatu | |||||||||
Makaranta |
Usmanu Danfodiyo University Faculty of Social Sciences (en) Jami'ar Jos | ||||||||
Matakin karatu | BSc Economics and Politics (en) | ||||||||
Harsuna |
Turanci Hausa Larabci Pidgin na Najeriya | ||||||||
Sana'a | |||||||||
Sana'a | ɗan siyasa | ||||||||
Imani | |||||||||
Addini | Mabiya Sunnah | ||||||||
Jam'iyar siyasa | Peoples Democratic Party |
Karatu gyara sashe
Bagudu Yayi digirin farko na Kimiyya (B.Sc.) a fannin tattalin arziki a Jami'ar Usman Dan Fodio da ke Jihar Sakkwato. Yana kuma da M.Sc. Ya karanta Economics a Jami'ar Jos ta Jihar Filato sannan ya yi digiri na biyu a fannin fasaha (M.A.) a harkokin kasa da kasa daga Jami'ar Columbia ta Amurka.[2]
Siyasa gyara sashe
An zaɓe shi a matsayin Sanata mai wakiltar mazabar Kebbi ta tsakiya a jihar Kebbi a Najeriya a zaɓen cike gurbi bayan da Sanata Adamu Aliero ya zama ministan babban birnin tarayya a watan Disambar 2008. Ya yi nasarar sake tsayawa takara a watan Afrilun 2011.zaɓen ƙasa gabada a tutar jam'iyyar People's Democratic Party (PDP).[3] A matsayinsa na Sanata, ya kasance memba a kwamitin majalisar dattawa kan ilimi (Majalisar Tarayya ta 6), kwamitin harkokin kasashen waje da kwamitin harkokin cikin gida.[4]
Ya zama dan takarar gwamna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Kebbi a zaɓen 2015 ya kuma lashe zaben sannan an rantsar da shi a matsayin gwamna a ranar 29 ga Mayun shekarar 2015.
Manazarta gyara sashe
- ↑ https://citizensciencenigeria.org/public-offices/persons/abubakar-atiku-bagudu
- ↑ https://www.premiumtimesng.com/opinion/596804-dear-president-elect-tinubu-please-avoid-atiku-bagudu-like-a-plague-by.html
- ↑ https://www.channelstv.com/tag/atiku-bagudu/
- ↑ https://www.manpower.com.ng/people/15449/abubakar-atiku-bagudu