Ummi Ibrahim

Jaruma kuma mawakiya

Ummi Ibrahim yar wasan Kannywood ce da ta shahara a fim din Jinsi inda ta samu suna Zeezee.[1][2]

Ummi Ibrahim
Rayuwa
Haihuwa Jihar Borno, 1987 (36/37 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Kanuri
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Sana'a
Sana'a Jarumi

Sana'a gyara sashe

Akwai cece-kuce game da jarumar a masana’antar kamar yadda ta ce ta fi ta. Wannan ya jawo martani a tsakanin abokan aikin ta tun bayan ganin ta na karshe a Kannywood a shekarar 2006.[3]

Rayuwa ta sirri gyara sashe

An yi ta raɗe-raɗin cewa Ummi ta hadu da tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida. Ta tabbatar da cewa har yanzu abokai ne a wata hira da wata jarida ta intanet.[4][5]

Jarumar Nollywood kuma tsohuwar budurwa ce ga Timaya, mawakin jihar Benue.[6]

An yaudari jarumar ne da ‘yan damfara miliyan 450 bayan wani mutum da ya fito a matsayin abokin kasuwanci ya kawo cinikin danyen mai. Masoya da abokan aikinta sun yi mata jaje tun lokacin da ta yi tunanin kashe kanta bayan lamarin.[7][8][9][10]

Ummi tayi alfahari da cewa bata sanya kayan kwalliya ba tunda kyawunta ya isa.[11]

Filmography gyara sashe

  • Yanayi[1]
  • Tutar Soyayya
  • Yan uwa
  • Gambiya
  • Jinsi

Duba kuma gyara sashe

Manazarta gyara sashe