Abu Zamira Mohammed shugaban ƙungiyar Boko Haram ne. Ya karɓi mulki ne bayan mutuwar Abubakar Shekau, kuma ya fara tattaunawa da gwamnatin Najeriya.[1] Ba a san matsayinsa na yanzu ba.

Abu Zamira
Rayuwa
Sana'a
Sana'a leader (en) Fassara

Mutuwar Shekau gyara sashe

Imam Liman Ibrahim ya sanar a cikin watan Agustan shekarar 2013 cewa ƙungiyar Boko Haram ta kori Abubakar Shekau saboda munanan hanyoyinsa. Ibrahim ya kuma sanar da naɗin Abu Zamira a matsayin da Shekau ya riƙe, da kuma kawo ƙarshen dabarun tashin hankali.[2]

Tattaunawar zaman lafiya gyara sashe

A watan Agustan 2013, Abu Zamira ya naɗa kansa da wasu mutane huɗu a matsayin wakilan Ƙungiyar Boko Haram a tattaunawar sulhu da gwamnatin Najeriya. Baya ga shi kansa tawagar ta haɗa da Abu Liman Ibrahim, Abu Adam Maisandari, Kassim Imam Biu da Malam Modu Damaturu. Waɗannan naɗe-naɗen sun kasance tare da ayyana tsagaita buɗe wuta na kwanaki 60, da kuma sanarwar cewa duk wani hari da aka kai da sunan Shekau bai inganta ba.[3]

Duba kuma gyara sashe

Manazarta gyara sashe