Solomon Ehigiator Arase (an haife shi 21 ga Yuni, shekara ta alif ɗari tara da hamsin da shida 1956) ɗan sandan Najeriya ne mai ritaya wanda ya yi aiki a matsayin Sufeto-Janar na ƴan sandan Najeriya na 18 (IGP) . Shugaban kasa Goodluck Jonathan ne ya nada shi IGP a shekarar 2015 bayan an tube Suleiman Abba . Kafin nadin sa a matsayin IGP, Arase ya kasance shugaban babban sashin tattara bayanan sirri na ‘yan sandan Najeriya, hukumar leken asiri da binciken manyan laifuka.[1]

Solomon Arase
Rayuwa
Haihuwa Sapele (Nijeriya), 21 ga Yuni, 1956 (67 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Harshen Edo
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Turanci
Harshen Edo
Pidgin na Najeriya
Sana'a

Rayuwa da aiki gyara sashe

An haifi Arase ranar 21 ga watan Yuni, 1956 a karamar hukumar Owan ta Yamma, jihar Edo a Kudancin Najeriya. Ya halarci Jami'ar Ahmadu Bello inda ya yi karatun digirinsa na farko kuma ya kammala karatunsa na digiri a fannin siyasa a shekara ta 1980. An dauke shi aikin ‘yan sandan Najeriya shekara guda bayan ranar 1 ga Disamba, 1981. Ya kuma sake samun digirin farko a fannin shari'a a Jami'ar Benin da kuma Masters daga Jami'ar Legas .

Yayin da yake aikin ‘yan sanda, Arase ya yi ayyuka da dama da suka hada da zama kwamishinan ‘yan sanda a jihar Akwa Ibom da kuma sashin tattara bayanan sirri a matsayin mataimakin sufeto Janar. Shi ma'aikaci ne a ƙwalejin Tsaro ta Najeriya kuma ya yi aiki a Namibia a lokacin aikin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.[2][3][4]


Arase ya yi ritaya daga aikin a ranar 21 ga Yuni na shekara ta, 2016. A ranar 21 ga watan Yuni, 2016, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Ibrahim Kpotum Idris a matsayin Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya . Bayan ya yi ritaya daga aikin ‘yan sanda, an nada Arase shugaban kwamitin da ke da alhakin aiwatar da dokar ƙungiyar ci gaban al’umma ta jiha a jihar Edo.[4][5][6] [7]

Manazarta gyara sashe

  1. Vanguard Newspaper. "Jonathan sacks Suleiman Abba, appoints Arase". Retrieved 28 April 2015.
  2. "Meet Nigeria's new Inspector General of Police, Solomon Arase | Premium Times Nigeria" (in Turanci). 2015-04-21. Retrieved 2022-03-17.
  3. "How I will spend the rest of my life — Ex-Police IG, Solomon Arase". Premium Times. Retrieved 9 September 2018.
  4. 4.0 4.1 Nnennah, Ibeh. "Meet Nigeria's new Inspector General of Police, Solomon Arase". Premium Times. Retrieved 10 September 2018.
  5. "Six DIG's to be retired as Arase bows out - Vanguard News". Vanguardngr.com. 2016-06-21. Retrieved 2016-08-07.
  6. "Buhari congratulates new Acting IGP Ibrahim Idris as Arase bows out - Vanguard News". Vanguardngr.com. 2016-06-21. Retrieved 2016-08-07.
  7. Funsho, Akinwale. "Former IGP, Solomon Arase, gets new job". Guardian. Retrieved 9 September 2018.