Geoffrey Jideofor Kwusike Onyeama (An haife shi ne a 2 ga watan Fabrairun shekarar ta 1956) ya kasance shi ne Ministan Harkokin Wajen Najeriya. Onyeama an nada shi Ministan Harkokin Wajen Najeriya ne a watan Nuwamba na shekarar ta 2015, Akarka shin Shugaba Muhammadu Buhari . [1]

Geoffrey Onyeama
Ministan harkan kasan waje

21 ga Augusta, 2019 - 2023
Ministan harkan kasan waje

11 Nuwamba, 2015 - 21 ga Augusta, 2019
Olugbenga Ashiru
Rayuwa
Haihuwa Enugu, 2 ga Faburairu, 1956 (68 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƴan uwa
Mahaifi Charles Onyeama
Ahali Dillibe Onyeama (en) Fassara
Karatu
Makaranta London School of Economics and Political Science (en) Fassara
Columbia University (en) Fassara
St John's College (en) Fassara
Harsuna Turanci
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Geoffrey Onyeama

Rayuwar farko da ilimi gyara sashe

Onyeama ya kasan ce ya fito daga dangin masanin shari'ar Najeriya Charles Onyeama.[2] Yayi digirinsa na farko, ya kuma Rike (BA) a Kimiyyar Siyasa daga Jami'ar Columbia, New York a shekarar ta 1977, ya kuma gama digirinsa na farko a bangaran Arts (BA), ya karanci Lauya a Kwalejin St John's College, Cambridge A shekara ta 1980. Yana da Digiri na biyu (LL. M) daga Makarantar Tattalin Arziki da Kimiyyar Siyasa ta London a shekarar ta 1982 , da kuma zama kwararre a bangaren Arts (MA) , da Shari'a daga St John's College, Cambridge a shekara ta 1984.[3] Onyeama an shigar da shi a matsayin Lauya na Kotun Koli ta Nijeriya a cikin shekarar ta1983 kuma an kira shi zuwa ga Ingilishi Bar na Grey's a shekarar ta 1981.[4]

Ayyuka gyara sashe

 
Geoffrey Onyeama

Onyeama ya fara aikin sa ne a matsayin Jami'in Bincike a Hukumar sake fasalin Dokokin Najeriya a Legas daga shekarar ta 1983 zuwa shekarar ta 1984. Sannan ya yi aiki a matsayin lauya tare da .Mogboh and Associate a Enugu, Nijeriya daga shekara ta 1984 zuwa ta 1985, A shekarar ta 1985, ya shiga Kungiyar World Intellectual Property Organization wato (WIPO) a matsayin Mataimakin Jami'in Shirye-shiryen ci gaban hadin gwiwa da alakar waje, Ofishin Afirka da Yammacin Asiya. Ya sami matsayi a WIPO ya zama Mataimakin Darakta Janar na sashen bunkasa a shekarar ta 2009. A watan Nuwamba na shekarar ta 2015 ne Shugaba Muhammadu Buhari ya nada shi Ministan Harkokin Wajen Najeriya.[5]

Rayuwar mutum gyara sashe

Onyeama ya yi aure; kuma yana da yara uku. da Matarsa ta yanzu ita ce Sulola; wanda Onyeama ke da yara biyu. da ita, Onyeama ya auri ɗiyar Christian Onoh : Nuzo Onoh kuma suna da ɗa na farko da matar. Onyeama mai suna Candice Onyeama; mai rubutun allo da shirya fim.[6][7][8]

 
Geoffrey Onyeama

A ranar 19 ga watan Yulin na shekara ta 2020, Onyeama ya shiga keɓewar likita bayan ya sanar da cewa ya samu tabbataccin COVID-19.[9] A ƙarshen watan Agusta na shekara ta 2020, Onyeama ya warke daga cutar COVID-19 na coronavirus; kuma ya koma aikinsa na jagoranci a matsayin HMFA: Mai girma Ministan Harkokin Waje a Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya.[10][11][12]

Duba kuma gyara sashe

Manazarta gyara sashe

  1. Ekott, Ini. "UPDATED: Buhari assigns Ministers; Fashola heads Power and Works, Amaechi gets Transportation". Premium Times. Retrieved 30 January 2016.
  2. "Geoffrey Onyeama: 7 Things You Should Know About Nigeria's Foreign Affairs Minister". Nigerian Monitor. Retrieved 30 January 2016.
  3. "CURRICULUM VITAE OF MR. GEOFFREY ONYEAMA" (PDF). Global Intellectual Property Center. Retrieved 30 January 2016.
  4. "CURRICULUM VITAE OF MR. GEOFFREY ONYEAMA" (PDF). Global Intellectual Property Center. Retrieved 30 January 2016.
  5. "The Honourable Minister of Foreign Affairs Mr. Geoffrey Onyeama". Ministry of Foreign Affairs of Nigeria. Archived from the original on 12 August 2016. Retrieved 30 January 2016.
  6. "Meet Geoffrey Onyeama and his Beautiful Wife Sulola". Nigeria Opera News. Archived from the original on 25 October 2021. Retrieved 20 September 2020.
  7. "Norwich Film Festival: Born Again Directed by Candice Onyeama". Norwach Film Festival: United Kingdom. Retrieved 20 September 2020.
  8. "Question and Answer With Candice Onyeama Director Screening Short Fiction Born Again". Barnes Film Festival: United Kingdom. Retrieved 20 September 2020.[permanent dead link]
  9. "Nigerian Foreign Minister Onyeama tests positive for coronavirus". July 19, 2020. Archived from the original on July 19, 2020. Retrieved November 24, 2020 – via af.reuters.com.
  10. "Foreign Minister Geoffrey Onyeama Recovers from Covid-19". The Guardian Nigeria. Retrieved 20 September 2020.
  11. "Foreign Minister Onyeama Recovers from COVID-19". Channels Television Nigeria. Retrieved 20 September 2020.
  12. "Foreign Minister Geoffrey Onyeama Recovers from COVID-19". Vanguard Nigeria News. Retrieved 20 September 2020.