Kanar Daniel Akintonde (an haife shi ranar 21 ga watan Nuwamban 1949) a Jihar Filato. Ya fito ne daga Ogbomoso dake Jihar Oyo.[1] An naɗa shi gwamnan soja a jihar Ogun ta Najeriya daga cikin watan Disambar 1993 zuwa watan Agustan 1996 a lokacin mulkin soja na Janar Sani Abacha.[2][3]

Daniel Akintonde
Gwamnan jahar ogun

9 Disamba 1993 - 22 ga Augusta, 1996
Olusegun Osoba - Sam Ewang (en) Fassara
Rayuwa
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Yarbanci
Karatu
Makaranta Jami'ar Tsaron Nijeriya
Harsuna Turanci
Yarbanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da soja

A 1994 Akintonde ya canza sunan Kwalejin Ilimi ta Jihar Ogun zuwa Kwalejin Ilimi ta Tai Solarin don girmama marigayi likita Tai Solarin.[4] Akintonde na daga cikin waɗanda aka kama da hannu a juyin mulkin watan Disamba na shekarar 1997.[5] An wanke shi daga tuhumar a ranar 20 ga watan Afrilun 1998.[6]

Ya yi ritaya daga aikin soja a cikin watan Yunin 1999, tare da dukkan jami’an da suka taɓa riƙe muƙamin minista, gwamnoni ko masu mulki a zamanin gwamnatin Babangida, Abacha da Abubakar.[7] A cikin watan Agustan 1999 ne Majalisar Dokokin Jihar Ogun ta gayyaci Akintonde domin ya amsa tambayoyi kan wasu kwangiloli da aka bayar a lokacin da yake mulki. An hana ƴan jarida shiga sauraron ƙarar.[8]

Manazarta gyara sashe

  1. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-02-03. Retrieved 2023-03-28.
  2. https://www.worldstatesmen.org/Nigeria_federal_states.htm
  3. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2022-08-10. Retrieved 2023-03-28.
  4. https://web.archive.org/web/20090625043236/http://www.tasuedu.org/tasuedweb/elibrary/docstore/TASUEDpub/Student%20Handbook
  5. https://www.unhcr.org/refworld/topic,4565c2252c,4565c25f389,3ae6ad056c,0.html
  6. http://www.unhcr.org/refworld/pdfid/3ae6a6924.pdf
  7. https://www.yahoo.com/
  8. https://web.archive.org/web/20110723204943/http://www.mediarightsagenda.net/other%20publications/Annuall%20Report%20for%201999.pdf