Ahmad Adamu Mu'azu CON (an haife shi ranar 11 ga watan Yunin 1955) ɗan siyasar Najeriya ne wanda ya yi gwamnan jihar Bauchi daga 1999 zuwa 2007.

Adamu Mu'azu
Gwamnan Jihar Bauchi

29 Mayu 1999 - 29 Mayu 2007
Abdul Mshelia - Isa Yuguda
Rayuwa
Haihuwa Jihar Bauchi, 11 ga Yuni, 1955 (68 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Haihuwa gyara sashe

Alhaji Ahmadu Adamu Mu'azu (an haife shi ranar 11 ga watan Yunin shekarata 1955) ya kasance gwamnan jihar Bauchi a Najeriya daga ranar 29 ga watan Mayun shekarar 1999 zuwa ranar 29 ga watan Mayun shekarar 2007. An naɗa shi shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, haifaffen garin Boto, ƙaramar hukumar Tafawa Ɓalewa a jihar Bauchi (a wancan lokacin na yankin Arewa),

Karatu gyara sashe

Mu’azu ya halarci makarantar firamare daga shekarar 1962 zuwa 1968. A tsakanin shekarar 1971 zuwa 1975 ya halarci makarantar sakandare ta Boy Gindiri da ke Jahar Binuwai-Plateau a lokacin inda ya samu digiri na ɗaya (Distinction) a jarrabawar kammala sakandare ta Afirka ta Yamma. Daga nan ya halarci Makarantar Koyon Ilimi ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, daga nan kuma ya samu digiri na farko a fannin Kimiyyar Kiwon Lafiyar Jama’a. Daga shekarar 1980 zuwa 1983 Mu'azu ya yi aiki a matsayin Manajan Sayoniya/Project Quantity Surveyor/Project Manager a Ma'aikatar Lafiya da Ma'aikatar Jin Daɗin Jama'a, Matasa, Wasanni da Al'adu a Jihar Kano. Ya koma makarantarsa a cikin shekarar 1983 kuma ya sami digiri na biyu a fannin Kimiyyar Gine-gine.

Aiki gyara sashe

Ya riƙe muƙamin manajan ƙadara na Kamfanin Haɓaka Kayayyakin Kaya na Jihar Bauchi kafin ya halarci Jami’ar Birmingham da ke Ƙasar Ingila inda ya sami digiri na biyu a fannin tattalin arziƙi na gine-gine. Daga shekarar 1984 har zuwa zaɓen sa a matsayin gwamnan jiha a shekara ta 1999, Mu'azu ya yi aiki a matsayin ɗan kasuwa a kamfanoni masu zaman kansu. A tsakanin shekarar 1984 zuwa 1987, ya kasance shugaban kwalejin kimiyya da fasaha ta tarayya dake Idah sannan kuma shugaban kamfanin gine-gine na Benue-Plateau dake Jos daga shekarar 1986 zuwa 1990. Ya kuma kasance mamba a hukumar bayar da tallafin karatu ta jihar Bauchi a wannan lokacin. A tsakanin shekarar 1987 zuwa 1997 ya yi ayyuka da dama da suka haɗa da daraktan hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya da kuma mamba a majalisar raya karkara ta jihar Bauchi. Ya samu kashi 56 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa a zaɓen gwamna na 1999 ya kuma hau mulki a ranar 29 ga watan Mayun 1999. An sake zaɓen shi a karo na biyu na shekaru huɗu a shekara ta 2003. Ya tsaya takarar kujerar majalisar dattawa a zaɓen 2007, amma ya sha kaye.

Siyasa gyara sashe

Ya taɓa zama shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa daga shekarar 2014 zuwa 2015.

Gwamnan Jihar Bauchi gyara sashe

A cikin watan Janairun shekarar 1999 Mu’azu ya tsaya takarar gwamnan jihar Bauchi a ƙarƙashin jam’iyyar PDP. An rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayun 1999.[1][2] An sake zaɓen shi gwamna a ranar 19 ga watan Afrilun 2003 da jimillar ƙuri’u 1,198,130.

Manazarta gyara sashe