Yaryasa
MYaryasa gari ne dake a ƙaramar hukumar Tudun Wada a Jihar Kano. Yaryasa na daga cikin Mazaba Goma sha ɗaya na ƙaramar hukumar Tudun Wada.[1][2]
Yaryasa | ||||
---|---|---|---|---|
mazaba a Najeriya | ||||
Bayanai | ||||
Ƙasa | Najeriya | |||
Wuri | ||||
| ||||
Ƴantacciyar ƙasa | Najeriya | |||
Jiha | jihar Kano | |||
Ƙaramar hukuma a Nijeriya | Tudun Wada |
Garin Yaryasa yana kan Titin Jos Wanda ya taso daga Kwanar Dan Gora.
Suna'ar mutanen garin yaryasa gyara sashe
Mutanen garin yaryasa sun ta allakane akan noma, kasuwanci da kamun kifi da ma aikatan gwamnati da yan siyasa.
Noman rani Dana damina shine babbar hanyar da suka dogara dashi, suna noma Masara, dawa, shinkafa, rake, Tumatir, albasa, kubewa, Tafarnuwa, dadai sauran Kayan Amfanin gona. Sannan akwai ma'adanai, dasuke tona daga rafikan dasuke zagaye dasu, ma'adanai sune kwallin kura,
Makarantun Garin gyara sashe
Sannan garin yaryasa yana dauke da makarantun zamani akwai firamare Guda hudu Acikin garin yaryasa, Sakandire ta maza karama da babba, sakandire ta yan mata karama da babba.
Tattalin Arziki gyara sashe
Garin yaryasa Yanada Arzikin kifi sakamakon yawan Rafuka da suke dashi. Sannan suna da babbar kasuwar siye da siyar da kifi danye,soyayye, da kuma gasashshe. Akwai kuma kasuwar sayar da kayan gwari wanda ake dauka akai Kudancin Najeriya. kamar Legas,Ibadan da warri