Vice Admiral Joseph Edet Wey (ya rayu daga Mayu 6, 1918 zuwa Disamba 12, 1991)[1] ya kasance hafsan sojin Ruwa ne a Nijeriya, yayi aiki a lokuta daban-daban, a matsayin sa na shugaban Nigerian Navy (wato Chief of Naval Staff),[2] da kuma Ministan Harkokin waje na wucin gadi,[3] sannan kuma ya zama Chief of Staff na Supreme Headquarters,[4] haka yasa ya zama de facto Mataimakin Shugaban Nijeriya lokacin janar Yakubu Gowon.

Joseph Edet Akinwale Wey
mataimakin shugaban ƙasar Najeriya

29 ga Yuli, 1966 - 29 ga Yuli, 1975
Babafemi Ogundipe (en) Fassara - Olusegun Obasanjo
Chief of Naval Staff (en) Fassara

1964 - 1973
Rayuwa
Haihuwa ga Maris, 1918
ƙasa Najeriya
Ƙabila Yarbawa
Mutuwa 12 Disamba 1990
Karatu
Harsuna Turanci
Yarbanci
Ibibio
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Digiri admiral (en) Fassara
Imani
Addini Kiristanci

Rayuwa da karatunsa gyara sashe

An haife shi a birnin Calabar a watan Maris shekarar 1918 a gidan Yarbawa da Ibibiyo/Efik wato mahaifinsa da mahaifiyar sa, Admiral Wey yayi karatunsa na farko a Calabar, Cross River State makarantar firamare na Methodist, Ikot Ekpene a Jihar Akwa Ibom a yanzu; sannan ya cigaba da karatunsa a Jihar Lagos. Ya fara aikin sa na farko a Marine Department a matsayin cadet kuma mai koyon zama injiya a 1940. A karshen koyon aikin sa a 1945, yayi aiki a dukkanin sea-going vessels dake a Marine Department. Lokacin da aka kirkiri Nigerian Navy a shekarar 1956, an maida shi bangaren Navy a matsayin sub-lieutenant. A 1962, an nada shi hafsa mai bada umurni na base da naval officer da ke rike da yankin Apapa, Lagos. A 1966, an nada shi Federal Commissioner na Establishment kuma ya zama mamba a federal Executive Council. An masa Karin girma da dama inda ya kai har zuwa matsayin vice-admiral.

Mukamai gyara sashe

mukaman da ya rike a soja sune:

  • Marine engineer, 1950
  • Sub-lieutenant and engineer, 1956
  • Lieutenant, 1958
  • Lieutenant commander, 1960
  • Captain, 1963
  • Commodore, 1964
  • Rear-admiral, 1967
  • Vice-admiral, 1971

Aje aiki/ritaya gyara sashe

Yayi ritaya a 1975 bayan samun juyin mulki da ta kawo Murtala Mohammed a shugaban cin kasa [4], wacce ta maye gurbin mulkin gwamnatin janar Yakubu Gowon. Ya rasu a 12 December 1991.[1]

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 Cite news|last1=Aginam|first1=Arthur-Martins|title=For Whom The Bell Tolls - Nigeria's first naval chief dies at 73|publisher=African Concord|date=December 1991
  2. Cite web |url= http://www.gamji.com/article6000/NEWS7030.htm%7Ctitle=Aburi: The "Sovereign National Conference" That Got Away |accessdate=2007-06-16 |work= Gamji|last=Siollun|first=Max|publisher=
  3. Cite web |url= http://www.time.com/time/magazine/article/0,9171,904219,00.html%7Ctitle=An[permanent dead link] Attentive Listener|accessdate=2007-06-16 |date=1970-03-02 |work= Time|publisher=Time Warner
  4. 4.0 4.1 Cite web |url= http://www.nigeriavillagesquare1.com/Records/2004/08/murtala-muhammeds-first-address-to.html%7Clast=Mohammed%7Cfirst=Murtala |title=Murtala Muhammed's First Address to Nigeria |accessdate=2007-06-16 |work=Nigeriavillagesquare.com |publisher=Nigerian Village Square