Jean Alingué Bawoyeu
Jean Alingué Bawoyeu (an haife shi a ranar 18 ga watan Agustan shekarar 1937 ), wanda aka sani da Faransanci a matsayin dattijo mai hikima, ɗan siyasan ƙasar Chadi ne da ya taba kasancewa Firayim Minista na Chadi daga shekarar 1991 zuwa 1992. A cikin shekarun 1970s, ya yi aiki a jere a matsayin Jakadan Amurka da Faransa. Daga baya, ya zama Shugaban Majalisar Kasa a shekarar 1990. Ya yi aiki a cikin gwamnatin a matsayin Ministan Shari'a daga shekarar 2008 zuwa 2010 ya kuma yi Ministan Wasiku da Sabbin Fasahar Bayanai daga shekarun 2010 zuwa 2013.
Jean Alingué Bawoyeu | |||||
---|---|---|---|---|---|
| |||||
Rayuwa | |||||
Haihuwa | Ndjamena, 18 ga Augusta, 1937 (86 shekaru) | ||||
ƙasa | Cadi | ||||
Ƴan uwa | |||||
Yara |
view
| ||||
Karatu | |||||
Harsuna |
Larabci Faransanci | ||||
Sana'a | |||||
Sana'a | ɗan siyasa da Mai wanzar da zaman lafiya | ||||
Imani | |||||
Jam'iyar siyasa | Union for Democracy and the Republic (en) |
Mabiyin addinin Kiristanci ne, kuma tushen goyon bayan sa shi ne yankin Tandjilé, a kudancin Chadi, inda ya zamo mahaifar sa.