Sanata Barau I Jibrin (an haife shi a shekarar 1959) ɗan siyasa ne ɗan Najeriya kuma mataimakin shugaban majalisar Dattawata ta 10, daga jihar Kano, Najeriya.[1][2]

Barau I Jibrin
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

13 ga Yuni, 2023 -
District: Kano North
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

11 ga Yuni, 2019 -
District: Kano North
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

9 ga Yuni, 2015 -
District: Kano North
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

29 Mayu 1999 -
District: Tarauni
Rayuwa
Cikakken suna Ibrahim Barau Jibrin
Haihuwa Kano, 1959 (64/65 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da ɗan kasuwa
Imani
Jam'iyar siyasa All Progressives Congress

Yana wakilcin Gundumar Arewa ta Kano. Sanata Barau shi ne tsohon Shugaban, Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yardajewa kuma tsohon Shugaban Kwamitin Sanatoci a Makarantun Sakandare da TETFUND a Majalisar Dattawa ta 8.[2]

Farkon rayuwa da ilimi gyara sashe

Barau I Jibrin, an haife shi a shekara ta 1959, kuma shi dan asalin garin Kabo ne, a karamar hukumar Kabo ta jihar Kano .

Yana da takardar shaidar digiri a fannin lissafi, takardar shaidar digiri a cikin Gudanar da Kasuwanci da farashi, takardar digiri na biyu akan Gudanarwa da Kasuwanci (MBA). Har'ila yau, yana riƙe da takardar shaidar a cikin Gudanar da Kasuwanci don yanke shawara game da kasuwanci daga babbar jami'ar Cornell, Amurka.

Bayan kammala karatun sa na farko, Sanata yayi aiki a takaice a sashen lissafi na Gidauniyar Kano, kafin ya yi murabus a shekarar 1992 don fara kasuwancinsa mai zaman kansa tare da fifikon masana'antu, inshora da kuma sassan tattalin arzikin Najeriya. Nasarar da ya samu a cikin kamfanoni sun shirya masa isasshe don fara aiwatar da abin da zai jawo hankalin mutanen sa ta hanyar amfani da siyasa.

Rayuwar Siyasa gyara sashe

Soyayyar Barau ga mutanensa ya sa shi yin takara a zaben shekarar 1999 zuwa Majalisar Wakilai don wakiltar mazabar Tarauni a majalisar Tarayya ta Jihar Kano, kuma yayi nasara. Yayin da yake a majalisar wakilai, ya yi aiki a matsayin Shugaban kwamitin lamuni kan Gidaje. Hakanan ya kasance memba a Kwamitin Wakilin Majalisar Wakilai kan mulki a waccan lokacin.

Bayan kammala aikinsa a majalisar wakilai, ya koma kan harkar kasuwancinsa kai tsaye, amma ba tare da ya ci gaba da sha'awar sa ba a harkar injiniyan siyasar Kano.

A shekarun baya, ya yi aiki a matsayin Shugaban Kamfanin Zuba Jari da Kayan Gida na Jihar Kano; kamfani ne da Gwamnatin Jihar Kano ta mallaka.

Ya taba zama Kwamishina Kimiyya da Fasaha a Jihar Kano. An nada shi a shekara ta 2001 don zama mamba a kwamitin da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya kafa domin sake nazarin tsarin Kasafin kudin Najeriya. A shekarar 2009, Gwamnatin Jihar Kano ta nada shi a matsayin mamba a Kwamitin Binciken Kasuwancin Jihar Kano; wani matsayi wanda ya sa aka sanshi sosai.

Bayan dawowar sa zuwa zaben fidda gwani a shekarar 2015, Sanata Barau ya tsaya takara ya kuma lashe zaben majalisar dattijai na Tarayyar Najeriya, wanda ya wakilci gundumar Sanatan Kano ta Arewa a karkashin inuwar jam'iyyar All Progressives Congress . An nada shi ne a wannan shekarar a matsayin Mataimakin Shugaban Kwamitin Rukunin Albarkatun Man Fetur (Downstream) na Majalisar Dattawa, daga baya ya zama Shugaban Kwamitin guda.

A shekarar 2016, aka sake shi a kwamitin Majalisar dattijai a makarantun sakandare da TETfund a matsayin Shugaban Kwamitin.

Kari a aiyukan sa na Majalisar Dattawa, shi memba ne a Kwamitin Yankin Neja Delta, Masana'antu, Sufuri na kasa.

Shine kuma Sakataren kungiyar Sanatocin Arewa.

Rayuwar kashin kai gyara sashe

Ya yi aure yana da yara.

Nasarori gyara sashe

Sanatan Arewa na shekara ta 2017 da na Sanatocin Majalisar Dattawan Najeriya.

Manazarta gyara sashe

  1. https://www.nassnig.org/mps/single/433
  2. 2.0 2.1 https://www.manpower.com.ng/people/15526/jibrin-barau