Hasumiyar Gobarau

Hasumiya a Katsina, Najeriya

Gobarau minaret ko a Hasumiyar Gobarau a Hausa ce. Gini ne mai kafa 50 a tsakiyar birnin Katsina, babban birnin jihar Katsina. Hasumiyar wani masallaci ne haka-zalika a matsayin Jami'a ce da aka gina a ƙarni na goma sha biyar a zamanin Sarkin Katsina, Muhammadu Korau (1348 – 1398 AD) [1] wanda shi ne Sarkin Musulmi na farko a tsohuwar masarautar Katsina. Asalin masallacin yana da nasaba da kokarin fitaccen malamin addinin musulunci Sheikh Muhammad Abdulkarim Almaghili. Almaghili wanda haifaffen Tlemcen ne a kasar Aljeriya ta yau,ya koyar na dan wani lokaci a Katsina lokacin da ya ziyarci garin a karshen karni na sha biyar a zamanin mulkin Muhammadu Korau.An gina masallacin Gobarau ne domin ya zama cibiyar ayyukan ruhi da tunani.Masallatai da aka samu a birnin Timbuktu sun yi wahayi zuwa gare shi a lokacin.[2]

Hasumiyar Gobarau
Hasumiya
Bayanai
Ƙasa Najeriya
Heritage designation (en) Fassara Declared National Monument (en) Fassara
Wuri
Map
 12°59′53″N 7°35′44″E / 12.997977°N 7.595517°E / 12.997977; 7.595517
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaJihar Katsina
BirniKatsina

Daga baya kuma an yi amfani da masallacin a matsayin makaranta. A farkon karni na 16, Katsina ta zama cibiyar kasuwanci da ilimi mai matukar muhimmanci a kasar Hausa,kuma masallacin Gobarau ya zama shahararriyar cibiyar ilimin addinin musulunci.Gobarau ya ci gaba da zama babban masallacin Katsina har zuwa farkon karni na 19 miladiyya lokacin da Sarkin Katsina Ummarun Dallaje(1805-1835)ya gina sabon masallaci,wanda daga baya Muhammadu Dikko(1906-1944)ya rushe,wanda ya gina shahararren Masallacin Dutsi(1906-1944).Babban Masallacin Katsina/Masallacin Juma'a na Kofar Soro),wanda har yau ake amfani da shi.

Sarkin Katsina Muhammadu Kabir Usman (1981–2008)ne ya gyara masallacin da hasumiyarsa.

Tatsuniyoyi gyara sashe

Shahararriyar tatsuniya game da asalin Gobarau ta nuna cewa lokacin da Muhammadu Korau ya kashe Jibda-Yaki Sanau,sarkin katsina na karshe,ya so ya gina masallaci.Bayan an zabo wurin ne sai aka samu matsalar alkiblar da masallacin zai fuskanta.Muhammadu Korau ya shawarci malaman addinin Musulunci na wancan lokacin,duk suka amince da wata alkibla,in ban da wani bafulatani mai suna Malam Jodoma.Sai gardama ta kaure,sai sauran malamai suka zagi Jodoma da cewa shi baqo ne mai son kawo rashin zaman lafiya.A fusace Malam Jodoma ya nufi wata hanya,sai ga Ka'abah ta bayyana a fili.An kuma yi amfani da hasumiya wajen hango sojojin da suka mamaye.

Muhammadu Korau ya yi mamaki,ya mai da Mallam Jodoma babban limaminsa, abin da ya ba wa sauran malamai mamaki,wanda har kishi ya sa Muhammadu Korau ya yi imani cewa Jodoma da ya yi suna yana son sarautarsa.An koro Jodoma daga Katsina,kuma ya sauka a kauyen Guga a karamar hukumar Bakori a jihar Katsina a yau,inda ya rasu.

Tsofaffin dalibai gyara sashe

Muhammad Ibn Muhammad Al-Fulani Al-Kishwani,Mathematician,Astrologer,Sufi

Wali Danmasani

Wali Danmarina

Yawon shakatawa gyara sashe

A yau Gobarau wurin shakatawa ne,tare da rijiyar Kusugu a Daura.

Tourism gyara sashe

A yau Gobarau wurin shakatawa ne, tare da rijiyan kusugu Dake daura.

Manazarta gyara sashe

  1. "About Us | Ministry Of Education Katsina". moekatsina.com. Archived from the original on 2023-06-17. Retrieved 2023-06-17.
  2. Shema, Abdulsalam. "ARCHITECTURAL HERITAGE AND CONSERVATION SITE, KATSINA GOBARAU MINARET". Cite journal requires |journal= (help)