Patricia Olubunmi Foluke Etteh (an haife ta ranar 17 ga watan Agusta, 1953)[1] ita ce Shugabar Majalisar Wakilan Nijeriya daga watan Yuni zuwa watan Oktoban shekara ta 2007.

Patricia Etteh
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

ga Yuni, 2011 -
District: Ayedaade/Irewole/Isokan
Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

6 ga Yuni, 2007 - 30 Oktoba 2007
Aminu Bello Masari - Dimeji Bankole
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

1999 -
Rayuwa
Haihuwa 17 ga Augusta, 1953 (70 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta University of Abuja (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Alliance for Democracy (en) Fassara
Peoples Democratic Party

Rayuwar mutum da ilimi gyara sashe

Etteh, Bayarabiya ce[2] an haife ta kuma a ranar 17 ga watan Agusta shekarar 1953.[1][3] Ta yi karatu akan gyaran gashi da kuma mai ilmin gyaran jiki, amma kuma ta samu digirin lauya daga Jami’ar Bukingham da ke Ingila kuma ta zama Lauyan Najeriya[4] a shekarar 2016.

Harkar siyasa gyara sashe

Etteh na wakiltar mazaɓar Ayedaade / Isokan / Irewole a jihar Osun Da farko an zaɓe ta a shekarar 1999 a matsayin mamba ta Alliance for Democracy (AD), amma ta sauya sheka zuwa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) lokacin da ta sake tsayawa takara a 2003. An zaɓe ta a matsayin kakakin majalisa gaba ɗaya ga watan Yunin 2007,[5] kuma ita ce mace tilo da ta taba rike wannan mukamin a cikin gwamnatin Najeriya.[6]

Badaƙalar cin hanci da rashawa gyara sashe

A watan Satumbar 2007, ta fuskanci wani kwamiti na 'ƴan majalisar kan zarge-zargen cewa ta ba da izinin kashe Naira miliyan 628 (kwatankwacin dalar Amurka miliyan 5) a kan gyaran gidanta da na mataimakinta, da kuma sayen motocin hukuma guda 12 da aka tanada don Majalisar Wakilai. An zarge ta da satar yayinda take ƙoƙarin yin magana a cikin majalisar, kuma an fitar da ita ta hanyar tsaro yayinda lamarin ya rikiɗe zuwa tashin hankali,[7] duk da cewa ba a gurfanar da ita a hukumance ba.

A hukumance PDP ta cigaba da mara wa Etteh baya, kodayake wasu mambobin, kamar Isyaku Ibrahim, sun soki wannan matsaya.[8] Marubuci kuma malami Wole Soyinka na daga cikin waɗanda suka yi kira da ta yi murabus,[9] yayinda tsohon Shugaban kasa kuma dan jam’iyyar PDP Olusegun Obasanjo ya cigaba da mara mata baya.[10] A ranar 30 ga Oktoba, bayan matsin lamba na makonni, Etteh ta yi murabus daga matsayinta na kakakin majalisa. [11] Mataimakin ta, Babangida Nguroje shi ma ya yi murabus. Koyaya a wurin zama na karshe na zaman majalisar wakilai karo na 6, an amince cewa "Babu wani rikodi ko cigaban majalisar inda aka taba gurfanar da Patricia Olubunmi Etteh,"[12]

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 "Etteh moves birthday party to US". Nigerian Tribune online. African Newspapers of Nigeria. 15 August 2007. Archived from the original on 26 September 2007. Retrieved 15 August 2007.
  2. Bamidele, Yemi (19 September 2007). "Adedibu – 'Etteh is Yorubas' Only Hope'". Daily Trust. Media Trust Limited, via allAfrica.com. Retrieved 20 October2007.
  3. "Honourable Patricia Etteh". NassNig.org. National Assembly of Nigeria. Archived from the original on 12 October 2007. Retrieved 7 October2007.
  4. "Former House of Reps Speaker, Patricia Etteh, among 4,225 new lawyers". Vanguard Online. Vanguard.
  5. "Homepage". The Nation Newspaper. Retrieved 8 March 2022.
  6. "Mark, Etteh, emerge Senate President, Speaker". IndependentNGonline.com. Daily Independent. 6 June 2007. Archived from the originalon 25 October 2007. Retrieved 15 August 2007.
  7. "Nigerian MPs brawl over speaker". BBC News. BBC. 20 September 2007. Retrieved 14 October2007.
  8. Izang, Atang (7 October 2007). "Etteh – PDP Endorsed Corruption – Isyaku Ibrahim". Leadership. Leadership Newspapers Group, via allAfrica.com. Retrieved 14 October 2007.
  9. Ekenna, Geoffrey (5 October 2007). "Resign, Soyinka tells Etteh". The Punch. Archived from the original on 15 July 2011. Retrieved 7 October2007.
  10. Nyam, Philip. "Etteh: Countdown To 16 October". Leadership. Leadership Newspapers Group. Archived from the original on 13 July 2011. Retrieved 14 October 2007.
  11. "Nigeria's parliamentary speaker quits over corruption scandal", Associated Press (International Herald Tribune), 30 October 2007.
  12. "Nigeria speaker goes in graft row" Archived 20 January 2016 at the Wayback Machine, BBC News, 30 October 2007.