Osita B. Izunaso (an haife shi 30 ga watan Oktoban shekarar 1966) an zaɓe shi a matsayin Sanata mai wakiltar Imo West (Orlu) na jihar Imo dake Najeriya, ya karɓi mulki a watan Yunin 2007. Ɗan jam’iyyar All Progressive Congress (APC) ne.[1]

Osita Izunaso
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

13 ga Yuni, 2023 -
Rochas Okorocha
District: Imo West
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

29 Mayu 2007 - 6 ga Yuni, 2011
Arthur Nzeribe - Hope Uzodimma
District: Imo West
Rayuwa
Haihuwa Imo, 30 Oktoba 1966 (57 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta University of Abuja (en) Fassara
Jami'ar Jos
Jami'ar Calabar
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Izunaso ya samu BA (Hons) daga Jami’ar Jos a cikin shekarar 1989, digiri na biyu a aikin jarida a Jami’ar Abuja a cikin shekarar 1998 da MBA daga Jami’ar Calabar (2002). An zaɓe shi a Majalisar Wakilai a shekarar 1992 da kuma a 1999, kuma an naɗa shi Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Shugaban Majalisar da Shugaban Majalisar Dattawa. Ya kasance Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Ministan Matasa da Wasanni daga 1995 zuwa 1997 kuma ya kasance Ministan Ƙwadago & Samar da Samfura daga shekarata 1998 zuwa 1999.[1]

Bayan ya hau kujerar sa a majalisar dattawa sai aka naɗa shi kwamitocin kan dokoki & kasuwanci, basussukan gida da waje, gidaje, iskar gas, harkokin waje da wasanni.[1] A wani nazari na tsakiyar wa’adi da Sanatoci suka yi a cikin watan Mayun shekarar 2009, Thisday ya bayyana cewa ya ɗauki nauyin ƙudirin dokar isar da ababen hawa, da jiyya da kula da waɗanda rikici ya rutsa da su, hukumar bunƙasa da adana harsunan gida a Najeriya da kuma Gyaran Dokar Bututun Mai. Ya ba da gudummawa ga muhawara gaba ɗaya kuma yana aiki a kwamitoci.[2] A matsayinsa na shugaban kwamitin da ke kula da iskar Gas shi ne ke da alhakin gudanar da bincike mai cike da cece-kuce kan wani gagarumin ƙarin kuɗin kwangilar aikin Escravos GTL daga dala biliyan 1.7 zuwa dala biliyan 5.9.[3]

A farkon shekarar 2009 ne aka yi yunƙurin dawo da Izunaso, inda al’ummar Mazaɓar Orlu Sanatan jihar Imo suka miƙawa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC.[4] Mataimakin shugaban majalisar dattawa , Ike Ekweremadu, ya yi watsi da barazanar da cewa ba shi da tushe balle makama, yana mai nuni da irin kyakkyawan aiki da Sanatan ya yi wa al’ummar jihar.[5] Izunaso da Ekweremadu na cikin ƙungiyar masu adawa da korar shugaban INEC Farfesa Maurice Iwu duk da ɗinbin matsalolin da aka fuskanta a zaɓen 2007. Ta yiwu Izunaso ya goyi bayan Imo saboda Imo ne ya ɗauki nauyin gudanar da zaɓen raba gardama kan kiran Izunaso.[6]

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 1.2 https://web.archive.org/web/20160303180713/http://www.nassnig.org/senate/member.php?senator=72&page=1&state=18
  2. https://allafrica.com/stories/200905250350.html
  3. https://allafrica.com/stories/201002120696.html
  4. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2009-07-16. Retrieved 2023-03-18.
  5. https://allafrica.com/stories/200902180221.html
  6. https://allafrica.com/stories/200903261008.html