Nasiru Muhammad Al -Muktar Kabara wanda aka fi sani da Nasuru Kabara (An haife shi a ranar 18 ga watan Afrilu, a shekara ta alif 1924 zuwa shekarata alif 1996),

Nasiru Kabara
Rayuwa
Haihuwa 1912
Mutuwa 1996
Sana'a

An haife shi a shekara ta alif 1924, kuma ya rasu a shekara ta alif 1996. Babban fitaccen malamin Addinin Musulunci na Ɗariƙar Qadiriyya ne a jihar Kano, wanda ya kafa Darul Qadiriyya, kuma Jagoran Qadiriyya na Ƙasashen Afirka ta yamma[1] a hukumance, Ɗansa Qaribullah Nasiru Kabara ne ya gaje shi bayan rasuwar sa. Kuma mahaifin wanda ake zargi da yin kalaman ɓatanci ga fiyayyen halitta Manzon Rahama (S A W), Abduljabbar Nasiru Kabara. Abduljabbar Nasiru Kabara wanda a yanzu haka gwamnatin jihar Kano a ƙarƙashin Abdullahi Umar Ganduje Khadimul Islam ta turashi zuwa gidan gyara hali a jihar Kano. Mal Nasiru Kabara yana ɗaya daga cikin fitattun Malaman addinin Musulunci a Najeriya da Africa a bangaren Ɗariƙar Qadiriyya.[1][2]

Rayuwar farko gyara sashe

An haife shi a Kuringawa a jihar Kano. Asali an ce kakansa ya fito daga tashar jiragen ruwa ta Kabara kusa da kogin Nijar, bayan Jihadin Usman dan Fodio a (1804-8). Daga nan ne ya yi hijira zuwa kasar Hausa, zuwa masarautar Kano a bayan ƙarni na goma sha takwas (18), inda ya zauna a gaban fadar masarautar Kano, inda aka ba shi fili don ya zauna, wanda yau an wayi gari ana kiran wajen da matsayin Kabara Ward "Unguwar Kabara".[3]

Ilimi gyara sashe

Nasiru Kabara ya sami mafi yawan iliminsa daga kawunsa kuma sanannen malamin Qadiriyya a wancan lokacin, wanda aka fi sani da Ibrahım Ahmad Al-kanawı Natsughünne, wanda yana ɗaya daga cikin fitattun malamai a Kano. Kawunsa da malaminsa sun yi hidimar sarki hudu daban -daban a matsayin mai ba da shawara kan Harker kin addini, daga cikinsu akwai Aliyu Babba, Abbas, Usman da Abdullahi Bayero, a lokacin kawun nasa yana daya daga cikin manyan membobin 'yan uwan Qadiriyya a garinsa.

Ya sanya ‘ya'yan Kabara zuwa rassa biyu na darika, wato Kuntiyya da Ahlulbaiti, wanda Shehu Usman Dan Fodio ya kafa.

Darika gyara sashe

Bayan kammala karatunsa a karshen karni na 1940s, Nasiru Kabara ya mai da hankali kan haɗa kan kungiyar Qadiriyya a Kano a karkashin jagorancinsa, daga nan ya cigaba da buɗe masallatai da dama a duk faɗin ƙasar Hausa a matsayin ɓangaren ƙadiriyya, wanda hakan ya sa kuma ya zama jagoran Qadiriyya a Afirka.

Musulunci gyara sashe

Shine wanda ya assasa Darul Qadiriyya (gidan Qadiriyya) a jihar Kano, inda dukkan mabiya Qadiriyya a duk fadin Afirka ta Yamma suka dauke ta a matsayin cibiyar Qadiriyya ta Yammacin Afirka, an ba shi taken Nasuru Kabara, Al-Sinhaji, Al-ibiadiri, Al-Maliki, Al-Ash'ari, Sarkin yakin Shehu Usmanu Bin Fodiyo.[4]

Harkar Qadiriyya gyara sashe

Rubutu gyara sashe

Ya rubuta litattafan musulunci da dama akan Tafseer da Hadisi, wanda aka ce sun kai littattafai sama da 300.

Iyali gyara sashe

Nasuru Kabara yana da 'ya'ya da yawa amma fitattu sune Qaribullah Nasiru Kabara babban ɗansa kuma magajinsa, ɗayan kuma Abduljabbar Nasuru Kabara.[5] sauran sun haɗa da

  • Sheikh Ibrahim Mu'azzam Nasir Kabara
  • Sheikh Sidi Musal Qasiyuni Nasir Kabara.
  • Malam Askiya Nasir Kabara
  • Malam Yahya Nasir Kabara
  • Malam Aburumana Nasir Kabara
  • Sayyidah Saratu Nasir Kabara
  • Sayyidah Nafisatu Nasir Kabara
  • Sayyidah Khudriyyah Nasir Kabara
  • Sayyidah Zam'atu Nasir Kabara 1
  • Sayyidah Saffanatu Nasir Kabara 1
  • Sayyidah Aishatu Mannubiyyah Nasir Kabara
  • Sayyidah Ummu Aimanal Habashiyyah Nasir Kabara (I)
  • Sayyidah Khadijatul Habashiyyah Nasir Kabara (II)
  • Sayyidah Huza'iyyah Nasir Kabara
  • Sayyidah Jamila Nasir Kabara
  • Sayyidah Bulkisu Nasir Kabara
  • Sayyidah Rukayya Nasuru Kabara
  • Sayyidah Hansa'u Nasir Kabara.

Duba kuma gyara sashe

  • Qaribullahi Nasiru Kabara

Haɗin waje gyara sashe

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 "Sheikh Nasir Muhammad Kabara". www.rumbunilimi.com.ng. Retrieved 2021-08-03. Cite error: Invalid <ref> tag; name ":0" defined multiple times with different content
  2. "Ku San Malamanku tare da Abduljabbar Kabara". BBC News Hausa. 2020-11-06. Retrieved 24 December 2021.
  3. "Teachings and writings of Nasuru Kabara" (PDF). Archived from the original (PDF) on 2021-08-06. Retrieved 2021-08-08.
  4. Tudun Nufawa, Abdulk̳adir Sammani; Sheshe, Aminu Ahmad (1997). Hasken Allah ba ya Gushewa: tarihin Sheikh Muhammad Nasuru Kabara, Al-Sinhaji, Al-K̳adiri, Al-Maliki, Al-Ash'ari, Sarkin Yak̳in Shehu Usmanu Bin Fodiyo (RA). Kano: The authors. OCLC 173037236.
  5. Malumfashi, Muhammad (2021-08-02). "An jirkita kalaman Abduljabbar – 'Yan Gidan Kabara sun zargi Malamai da sharri". Legit.ng - Nigeria news. Retrieved 24 December 2021.