Ja'afar Mahmud AdamAbout this soundJa'afar Mahmud Adam  An haife shi a ranar 12 ga watan Fabrairu, shekara ta alif ɗari tara da sittin 1960) ya bar duniya a ranar 13 ga watan Afrilu, shekara ta 2007). An Haifeshi a garin Daura ne ta jahar Katsina amma ya girma a birnin Kano. Ya rasu ne sanadiyar harbin bindiga daga wasu da ba'a san ko su waye ba, sun harbe shi a lokacin da yake sallar Asubahi a masallaci a garin birnin Kano a Unguwar Ɗorayi, Malamin Addinin Musulunci ne, Ahlus-Sunnah ma'ana: mabiyin kungiyar Jama'atu Izalatul Bid'ah Wa Ikamatus Sunnah Izala ne a najeriya ƙungiyar Addinin Musulunci da take ƙoƙarin kawar da Bidi'a (wato ibadun da basu da tushe a Musulunci) da tabbatar da sunna ta ma'aiki manzon Allah SAW, wanda babban cibiyan kungiyar ta ke a garin Jos. Bayan haka ya kasance mallamin Tafsirin Al-Kur'ani mai girma. sannan za'a iya cewa shi ne jagoran salafawa-sunna a Najeriya.

Ja'afar Mahmud Adam
Rayuwa
Haihuwa Daura, 12 ga Faburairu, 1960
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Mutuwa Kano, 13 ga Afirilu, 2007
Yanayin mutuwa kisan kai
Karatu
Makaranta Jami'ar Musulunci ta Madinah
Harsuna Turanci
Hausa
Larabci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a Mai da'awa
Imani
Addini Mabiya Sunnah
Sheikh

Ja'afar Mahm
Ja'afar Mahmud Adam
Title Sheikh Ja'afar Mahmud Adam
Personal
Haihuwa
Ja'afar Mahmud Adam

Fabrairu 12,1960
Mutuwa Afirilu 13, 2007
Sababin mutuwa Kisan gilla
Makwanci Kano
Addini Islam
Dan kasan Najeriya
Kabila Hausa
Era Zamanin nan
Yanki Arewacin Najeriya
Reshan addini Sunna and Salafiyya[1]
Mazhabi Malikiyya
Dabbaga Malikiyya
Aiki mafi so Hadisi, Tafsiri and Tauhidi
Babban tinani Kawar da bidi'a
Sana'a Wa’azi
Muslim leader
Tarbiyya a Abubakar Mahmud Gumi.

Tarihin sa gyara sashe

Karatunsa gyara sashe

Ya hardace Al-ƙur'ani a shekara ta alif ɗari tara da saba'in da takwas 1978[2].

Koyarwa gyara sashe

Sheik Ja'afar yana yin wa'azi a masallacin Indimi a birnin Maiduguri wanda yake samun halartar mataimakin gwamnan jahar Borno.

Rasuwarsa gyara sashe

An kashe Sheikh Ja'afar Mahmud Adam ne a masallacinsa da ke unguwar Ɗorayi cikin birnin Kano wanda take Arewacin Najeriya a watan Afrilu na shekarar dubu biyu da bakwai 2007.

Duba nan gyara sashe

Manazarta gyara sashe

  1. Gérard L. F. Chouin, Religion and bodycount in the Boko Haram crisis: evidence from the Nigeria Watch database, p. 214. 08033994793.ABA
  2. Ana jimamin cika shekara 13 da kisan Sheikh Jafar, BBC Hausa, ran 13 ga Afrilu a shekara ta 2020.