Dauda Kako Are

Dan siyasar najeriya

Dauda Kako Are (an haifeshi ranar 11 ga watan Yuli, 1959)[1] akawu ne kuma ɗan siyasa. Dan Majalisar Wakilan Najeriya ne mai wakiltar mazaɓar Mushin I bayan ya zama zakara a zaɓen Najeriya na 2015 a watan Afrilu a ƙarƙashin jam'iyyar Accord Party.[2][3]

Dauda Kako Are
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

9 ga Yuni, 2015 - 9 ga Yuni, 2019
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

6 ga Yuni, 2011 - 4 ga Yuni, 2015
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

5 ga Yuni, 2007 - 6 ga Yuni, 2011
Rayuwa
Haihuwa Lagos, 11 ga Yuli, 1959 (64 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Jami'ar Lagos Digiri a kimiyya : accounting (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da accountant (en) Fassara
Imani
Jam'iyar siyasa Action Alliance (en) Fassara

Rayuwar farko da ilimi gyara sashe

An haifi Kako Are, ranar 11 ga watan Yuli, na shekara ta alif ɗari tara da hamsin da tara 1959, a birnin Lagos na Najeriya. Ya halarci Makarantar Sakandare ta Baptist, Saki, Jihar Oyo inda ya samu shaidar kammala karatunsa na Senior School a shekara ta alif ɗari tara da saba'in da bakwai 1977. Ya wuce Jami'ar Legas, Akoka inda ya yi digirinsa na farko a fannin (Accounting) a shekarar alif ɗari tara da tamanin da biyar 1985.

Fagen Siyasa gyara sashe

Kako Are dai ya fara harkar siyasa ne a shekarar alif ɗari tara da casa'in da tara 1999 bayan an zaɓe shi a matsayin wakilin mazaɓarsa a majalisar dokokin jihar Legas daga 1999 zuwa 2003 ƙarƙashin inuwar jam'iyyar Action Congress of Nigeria. Ya tsaya takarar majalisar wakilai ta tarayya a ƙarƙashin jam’iyyar Accord Party (A) kuma ya lashe zaɓen a matsayin mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Mushin I a babban zaben Najeriya na 2015.

Manazarta gyara sashe

  1. Nigeria, Media (2018-06-05). "Biography Of Dauda Kako Are". Media Nigeria (in Turanci). Retrieved 2020-07-08.
  2. Admin (2016-11-15). "ARE,Hon. Abayomi Dauda Kako". Biographical Legacy and Research Foundation (in Turanci). Retrieved 2020-07-08.
  3. "Rep attributes victory to confidence, trust of electorate". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2015-04-14. Retrieved 2020-07-08.