Daouda Malam Wanké (6 ga Mayun shekarar 1946 - 15 ga Satumbar 2004) ya kasance soja da shugaban siyasa a Nijar. Ya kasance ɗan ƙabilar Hausa.

Daouda Malam Wanké
shugaban Jamhuriyar Nijar

11 ga Afirilu, 1999 - 22 Disamba 1999
Ibrahim Baré Maïnassara - Mamadou Tandja
Rayuwa
Haihuwa Yelou, 6 Mayu 1946
ƙasa Nijar
Mutuwa Niamey, 15 Satumba 2004
Karatu
Harsuna Faransanci
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da soja
Mamba Conseil du Salut National (en) Fassara
Conseil de Réconciliation Nationale (en) Fassara
Imani
Jam'iyar siyasa National Movement for the Development of Society (en) Fassara

Ana taƙaddama game da shekarar haihuwar Wanké. Yawancin kafofin suna da'awar cewa 1954 ne [1] yayin da wasu 1946. [2]

Tarihin rayuwa gyara sashe

An haife shi a Yellou, wani gari kusa da babban birnin Nijar, Yamai. Ya shiga aikin sojan Nijar, har ya kai matsayin Manjo. A ranar 9 ga Afrilun shekarata 1999, Wanké ya jagoranci juyin mulkin soja inda aka kashe Shugaba Ibrahim Baré Maïnassara, wanda shi da kansa ya hau kan mulki a wani juyin mulkin soja. [3] [4] Tsawon kwanaki biyu da rashin tabbas na siyasa sosai a Nijar, kamar yadda Firayim Minista, Ibrahim Hassane Mayaki da wasu da dama su ma suka yi ikirarin shugaban. A ranar 11 ga Afrilun shekarar 1999, Wanké ya zama shugaban kasa, yana shugabancin gwamnatin rikon kwarya da ta yi alkawarin gudanar da zabe a karshen shekarar. [5]

Gwamnatin Wanké ta cika alkawarinta, kuma ta mika mulki ga sabon zaɓaɓɓen shugaban ƙasar, Mamadou Tandja, a cikin Disamba 1999. Daga baya Wanké ya sha wahala daga matsaloli daban-daban na lafiya, gami da matsalolin zuciya da hawan jini. A watannin karshe na rayuwarsa, ya yi tafiya zuwa Libya, Morocco da Switzerland don neman lafiya. Ya mutu a Yamai. Ya bar mata daya da yara uku.

Manazarta gyara sashe