Niamey
Niamey babban birnin ƙasar Nijar ne. Wannan birnin yana a matsayin babbar gundumar Birni kuma ya hada gunduma biyar ne. Bisa ga ƙidayar jama'a a shekarar 2011, jimillar mutane 1,302,910 (miliyan ɗaya da dubu dari uku da biyu da dari tara da goma). An gina birnin Niamey a farkon karni na ashirin bayan haifuwan annabi Issa. Babban kogin nan na "Niger" wanda cibiyarshi take tsakanin Sierra Leone da Guinée, ya ratsa birnin Niamey.
![]() | ||||
---|---|---|---|---|
Ɲamay (mis) Yamai (ha) ⵏⵉⴰⵎⵢ (mis) | ||||
![]() | ||||
| ||||
Wuri | ||||
| ||||
Jamhuriya | Nijar | |||
Babban birnin | ||||
Yawan mutane | ||||
Faɗi | 1,026,848 (2012) | |||
• Yawan mutane | 4,291.05 mazaunan/km² | |||
Labarin ƙasa | ||||
Yawan fili | 239,300,000 m² | |||
Wuri a ina ko kusa da wace teku | Nijar | |||
Altitude (en) ![]() | 207 m | |||
Tsarin Siyasa | ||||
• Gwamna |
Barry Bibata Niandou (en) ![]() | |||
Bayanan Tuntuɓa | ||||
Kasancewa a yanki na lokaci | ||||
Lamba ta ISO 3166-2 | NE-8 |
Wannan mukalar bata da Reference (Manazarta) ko daya, ka taimaka ta hanyar samar da Manazarta daga littafi ko yanar gizo, duba wannan shafin domin samun masaniya akan yanda zaka samar da Reference (Manazarta) a cikin wannan mukalar.
![]() |


Tarihi gyara sashe
Birnin Niamey ya fara ci gaba ne wajen shekarar 1900, a daidai wani waje inda Fulanin Koira, Gaweye, Kalley, Maourey, Zongo, Gamkalé da Saga suke a lokacin. Kabilar da tafi yawa sune Zabarmawa ko kuma Songhai. Turawa sun iso Niamey ne a makare saboda tana can yammacin kasar inda babu wani kasuwanci da akeyi. Mutanen Gurmance (Gourmantché) ne suka fara rayuwa a yankin Niamey. Amma, wadanda suka kafa kauyen Niamey, Arawa ne da suka zo daga Matankari.