Susana Adam ‘yar siyasa ce ‘yar kasar Ghana wacce ta taba zama ‘yar majalisar wakilai a mazabar Mamprusi ta Yamma daga 1997 zuwa 2001.[1]

Susana Adam
Member of the 2nd Parliament of the 4th Republic of Ghana (en) Fassara

7 ga Janairu, 1997 - 6 ga Janairu, 2001
District: Walewale Constituency (en) Fassara
Election: 1996 Ghanaian general election (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Ghana
ƙasa Ghana
Karatu
Harsuna Turanci
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Ta tsaya takarar kujerar West Mamprusi a kan tikitin jam'iyyar National Democratic Congress (NDC) a lokacin zaben 'yan majalisa na 1996 kuma ta samu kuri'u 23,021 wanda ke wakiltar kashi 63% na dukkan kuri'un da aka kada.[2] A lokacin zaben ‘yan majalisa na 2000, ta sha kaye a hannun Issifu Asumah na jam’iyyar PNC. Ta samu kuri'u 12,735 (37.3%) yayin da Asumah ta samu kuri'u 18,907 (55.4%).[3] A cikin 2004, duk da cewa ta sami babban goyon baya daga jam'iyyar NDC mai aminci kafin babban zaben, Alidu Iddrisu Zakari ya wakilci jam'iyyar don yin takara a sabuwar kujerar Walewale ta Gabas. Sakamakon haka Zakari ya doke Issifu Asumah ne a zaben majalisar dokoki na shekara ta 2004.[4]

Duba kuma gyara sashe

Manazarta gyara sashe

  1. Larvie, John; Badu, K. A. (1996). Elections in Ghana 1996, part 2. p. 152. ISBN 9789988572495.
  2. Larvie, John; Badu, K. A. (1996). Elections in Ghana 1996, part 2. p. 152. ISBN 9789988572495.
  3. Ephson, Ben (2003). Countdown to 2004 Elections:Compilation of All the Results of the 1996 & 2000 Presidential & Parliamentary Elections with Analysis. Allied News Limited. p. 218. ISBN 9789988016418. Retrieved 20 May 2020.
  4. "Susana Adam Elected to Contest Mamprusi West Constituency". www.ghanaweb.com. Retrieved 20 May 2020.