Mariama Keita (1946 - 29 Oktoban shekarar 2018) mace ta farko a Nijar ƴar jarida ce kuma mai fafutukar mata.[1]

Mariama Keita
Ɗan Adam
Bayanai
Jinsi mace
Ƙasar asali Nijar
Suna Mariama
Sunan dangi Keïta (en) Fassara
Shekarun haihuwa 1946
Wurin haihuwa Niamey
Lokacin mutuwa 29 Oktoba 2018
Wurin mutuwa Istanbul
Harsuna Faransanci
Sana'a ɗan jarida, gwagwarmaya da Mai kare hakkin mata
Mai aiki Voix du Sahel (en) Fassara
Muƙamin da ya riƙe shugaba

Tarihin Rayuwa gyara sashe

An haifi Keita a shekara ta 1946 a Yamai. Ta fara ne a matsayin edita kuma mai gabatar da jarida da kuma gidan rediyon jama'a na La Voix du Sahel. A shekarar 1993, ta shiga cikin yaɗa kundin tsarin mulkin Nijar, wanda ya ba da damar gudanar da zaɓen dimokuraɗiyya na farko a ƙasar.[2]

Daga shekara ta 2003 zuwa 2006, Keïta ta kasance shugaban majalisar ƙoli ta sadarwa (CSC), hukumar da ke da alhakin tsara kafofin yaɗa labaran ƙasar. A cikin shekarunta na ƙarshe na aikinta, ta yi aiki a matsayin darektan La Voix du Sahel. Ita ce ƴar Nijar ta farko da ta zama ƴar jarida a daidai lokacin da ake ɗaukar wannan sana’a ga maza kaɗai a Nijar.[3]

Mace mai fafutuka kuma mai kishin mata, ta kasance majagaba wajen kare haƙƙin mata a Nijar. Ita ce mai kula da ƙungiyoyi masu zaman kansu da ƙungiyoyin mata a Nijar, rukunin gine-gine kusan hamsin.[4] Ita ce kuma shugabar ɗaya daga cikin ƙungiyoyi masu zaman kansu na farko a ƙasar, wato Association for Democracy, Freedom and Development.[3][5]

Mutuwa gyara sashe

Keita ta rasu ne a ƙasar Turkiyya a ranar 29 ga watan Oktoban shekarar 2018, tana da shekaru 72 a duniya, sakamakon doguwar jinya.[6]

Manazarta gyara sashe