Mahmud Mohammed, CON, OFR (an haife shi 10 Nuwamba shekara ta alif ɗari tara da arba'in da shida1946A.c). masanin shari'a ne dan Najeriya kuma tsohon Alkalin Alkalan Najeriya.[1][2][3]

Mahmud Mohammed
Chief Justice of Nigeria (en) Fassara

2014 - 2016
Rayuwa
Haihuwa Jalingo, 10 Nuwamba, 1946 (77 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a mai shari'a

Kuruciya gyara sashe

An haifi Mai shari'a Mohammed a ranar 10 ga watan Nuwamba 1946.,a Jalingo babban birnin jihar Taraba arewa maso gabashin Najeriya.[4] Ya sami digiri na farko a fannin shari'a a Jami'ar Ahmadu Bello a shekarar 1970, kuma aka kira shi zuwa kungiyar lauyoyin Najeriya, a shekarar da ya kammala makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya.[5]

Aikin shari'a gyara sashe

Ya shiga aikin shari’a a lokacin tsohuwar jihar Arewa maso Gabas a matsayin lauya, kuma a shekarar 1991, ya zama babban alkalin alkalan jihar Taraba, a shekarar ne aka tabbatar da nadinsa a matsayin babban alkalin jihar.[6] A 2005, an nada shi mai shari'a a Kotun Koli ta Najeriya.[7] A watan Nuwamba 2014, an nada shi a matsayin Alkalin Alkalan Najeriya ya gaji Aloma Mariam Mukhtar, mace ta farko a Najeriya.[8] Mai shari'a Mahmud Mohammed shine shugaban majalisar shari'a ta kasa.[4]

Kungiyoyi gyara sashe

  • Memba, Kungiyar Lauyoyin Najeriya
  • Memba, gungiyar Lauyoyin Duniya
  • Memba, Kungiyar Benchers ta Najeriya
  • Memba, Majalisar Shari'a ta Kasa

Manazarta gyara sashe

  1. "TVC NEWS - Justice Mahmud Mohammed - Magistrate judges - Nigeria - TVC NEWS". tvcnews.tv. Retrieved 28 April 2015.
  2. "CJN warns judges against scuttling 2015 polls". The Punch - Nigeria's Most Widely Read Newspaper. Archived from the original on 28 April 2015. Retrieved 28 April 2015.
  3. "Jonathan, others honour fallen heroes". The Punch - Nigeria's Most Widely Read Newspaper. Archived from the original on 25 June 2015. Retrieved 28 April 2015.
  4. 4.0 4.1 "FJSC Nominates Mahmud Mohammed as Next CJN, Articles - THISDAY LIVE". thisdaylive.com. Retrieved 28 April 2015.
  5. "Justice Mahmud Mohammed". Vanguard News. Retrieved 28 April 2015.
  6. "Jonathan approves Justice Mahmud Mohammed as next CJN". DailyPost Nigeria. Retrieved 28 April 2015.
  7. OUR REPORTER. "The man Justice Mahmud Mohammed". The Nation. Retrieved 28 April2015.
  8. "Mahmud Mohammed: The new Chief Justice of Nigeria". Daily Independent, Nigerian Newspaper. Retrieved 28 April 2015.

Template:Chief Justices of Nigeria