Junior Noubi Fotso (an haife shi a ranar 20 ga watan Yunin shekarar 1999) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne na Gabon wanda ke taka leda a matsayin ɗan wasa mai tsaron gida ga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Championnat National 2 club Vannes da kuma ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Gabon. [1] [2]

Junior Noubi Fotso
Rayuwa
Haihuwa Libreville, 20 ga Yuni, 1999 (24 shekaru)
ƙasa Gabon
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
 

Ayyukan kasa da kasa gyara sashe

Noubi Fotso ya fara buga wa tawagar kasar Gabon wasa a wasan sada zumunci da Burkina Faso da ci 3-0 a ranar 2 ga watan Janairu, 2022. An zabe shi ne a gasar cin kofin Afrika na shekarar 2021 da aka gudanar a Kamaru a watan Janairu da Fabrairu 2022.[3]

Manazarta gyara sashe

  1. Junior Noubi Fotso at Soccerway
  2. Junior Noubi Fotso at National-Football-Teams.com
  3. Le Sauce, Arnaud (27 December 2021). "Football. Noubi Fotso à la CAN, Pétrel titulaire en Coupe de France face au Paris SG" [Football. Noubi Fotso at AFCON, Pétrel starting in the Coupe de France against Paris SG]. Le Télégramme (in French). Retrieved 29 April 2022.