Cordelia Ainenehi Agbebaku (Janairu, 1961 – Fabrairu 16, 2017) Malamar Najeriya ce kuma tsohuwar mataimakiyar shugaban jami'ar Alli Ambrose.

Rayuwa gyara sashe

An haifi Agbebaku a Ekpoma a watan Janairu, 1961. Ta yi karatun shari'a a Jami'ar Jihar Bendel a yanzu Ambrose Alli University, Ekpoma.[1] Agbebaku ta zama mataimakiyar shugaban jami’ar Ambrose Alli (AAU) a hukumance a shekarar 2014 lokacin da gwamna Adams Oshiomhole ya tabbatar da naɗin nata.[2] Ta kasance tana aiki a matsayin mai riko tun a shekarar 2011 yayin da take aiki a matsayin shugabar tsangayar doka.[1] Agbebaku ta rasu ne a ranar 16 ga watan Fabrairu, 2017, a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Benin, kuma ta bar ‘ya’ya da mijinta Farfesa Phillip Agbebaku na sashen kimiyyar siyasa a jami’ar.[3]

Duba kuma gyara sashe

  • Jerin mataimakan shugabannin jami'o'i a Najeriya

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 "History of Ambrose Alli University, Ekpoma". Archived from the original on 3 February 2014.
  2. "Appointment of a Substantive Vice-Chancellor For Ambrose Alli University, Ekpoma".
  3. Okere, Alexander. "Ex- AAU VC,Prof. Agbebaku, dies at 55". Punchng.