A ranar 3 ga watan Yunin shekarar 2021, wasu ‘yan bindiga sun kai hari a ƙauyuka takwas a jihar Kebbi, arewa maso yammacin Najeriya, inda suka kashe akalla mutane 90.

Infotaula d'esdevenimentKisan kiyashi a Kebbi, 2021
Iri harin ta'addanci
Kwanan watan 3 ga Yuni, 2021
Wuri Kebbi
Ƙasa Najeriya
Adadin waɗanda suka rasu 90

Faruwar Lamarin gyara sashe

An fara kai harin ne da karfe 3 na rana; ‘ Yan bindigar da suka hau babura sun kai farmaki kauyukan Koro, Kimpi, Gaya, Dimi, Zutu, Rafin Gora da kuma Iguenge.[1][2] ‘Yan bindigar sun fito ne daga jihohin Niger da Zamfara da ke makwabtaka da Najeriya, sun kuma yi awon gaba da shanu tare da lalata amfanin gona.[1][3][4]

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 Attackers kill 88 people in northwestern Nigeria edition.cnn.com
  2. "Gunmen attack villages, kill over 90 in Nigeria". DW. Retrieved 27 June 2021.
  3. "Bandits kill 88 in Kebbi". guardian.ng. 5 June 2021.
  4. "Cattle thieves kill 88 in northwest Nigeria massacre". www.theweek.in.