Yankin Yamma ta Tsakiya, Najeriya

Yankin Tsakiyar-Yamma ya kasance rabon Najeriya daga shekarar 1963 zuwa 1991, daga 1976 ana kiranta da Bendel state.

Yankin Yamma ta Tsakiya, Najeriya

Wuri
Map
 6°19′03″N 5°36′52″E / 6.3175°N 5.6144°E / 6.3175; 5.6144

Babban birni Kazaure
Bayanan tarihi
Mabiyi Western Region (en) Fassara
Ƙirƙira ga Yuni, 1963
Rushewa 27 Mayu 1967

An kafa shi a watan Yunin 1963 daga Benin da lardunan Delta na Yammacin Yankin, kuma babban birninta shi ne Benin City . An kuma sake canza mata suna zuwa lardi a shekara ta 1966, kuma a shekarar 1967 lokacin da aka raba sauran lardunan zuwa jihohi da yawa, ya ci gaba da kasancewa yanki yanakke, ya zama jiha.

A lokacin yakin basasar Najeriya, sojojin Biafra sun mamaye sabuwar kasar ta Mid-Western, akan hanyarsu ta zuwa Lagos, a kokarin tilasta kawo karshen yakin cikin gaggawa. Yayin da yake karkashin mamayar Biafra, an ayyana jihar a matsayin " Jamhuriyar Benin ". Yayin da sojojin Najeriyar suka sake kwace yankin, jamhuriya ta ruguje ne kwana daya kacal bayan sanarwar lokacin da sojojin Najeriyar suka kame garin Benin.

A shekarar 1976 aka sake yiwa jihar suna Bendel . An raba shi zuwa jihar Delta da Edo a cikin 1991. [1][2]

Yawan jama'a gyara sashe

Yankin ya kunshi tsoffin lardunan Benin da Delta. Lardunan Benin suna da masu magana da yaren Edo yayin da lardin Delta ke da Ijaws, Isekiri, Urhobo, Isoko da Ukwuani masu magana ban da Ika da Aniocha.[3]

Tattalin arziki gyara sashe

Yankin yana da katako da masana'antar roba a Sapele wanda shima tashar jiragen ruwa ke tallafawa. Bugu da kari, ta samar da kayayyakin dabino, masara, wake da sauran kayan abinci don amfanin gida. A cikin lardin Kudancin Delta, an kuma gano mai kuma an sanya shi don amfanin yankin.[4]

Manazarta gyara sashe

 

  1. http://logbaby.com/encyclopedia/history-of-delta-state_10219.html#.UqzIAfTuIQo
  2. "Mid Western Region, Nigeria (1963-1966)".
  3. "Mabinuori, Lai (July 13, 1963). "Who are the Mid-West People". Daily Times (Nigeria).
  4. 'Ojiako, James (July 13, 1963). "Mid-West Economy Promising". Daily Times (Lagos).