Olasunkanmi Abioye Opeola, Kurunloju I

Sarkin gargajiya, na garin Yarbawa na Iroko, Jihar Oyo, Najeriya.

Olasunkanmi Abioye Opeola, Kurunloju I (an haife shi ranar 9 ga watan Maris, 1961) Oniroko ne, ko kuma basaraken gargajiya, na garin Yarbawa na Iroko, Jihar Oyo, Najeriya. Ya yi mulki tun ranar 4 ga watan Fabrairun 2011.[1]

Olasunkanmi Abioye Opeola, Kurunloju I
Rayuwa
Haihuwa 9 ga Maris, 1961 (63 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a

Rayuwar farko gyara sashe

An haifi HRH Oba Olasunkanmi, ranar 9 ga watan Maris Shekara ta 1961, a gidan sarautar Abioye. Shine Oniroko/Sarki na farko daga gidan sarautar Abioye.[2]

Karatu gyara sashe

Olasunkanmi ya halarci Makarantar Grammar ta Iroko, Iroko, sannan ya wuce Kwalejin Malamai ta St’ Andrew’s, Iseyin a shekarar 1979, inda ya samu takardar shaidar Grade II a shekarar 1982. Ya shiga hidimar koyarwa ta jihar Oyo a shekarar 1983, kuma ya halarci kwalejin ilimi ta Ikere-Ekiti daga shekarar 2000 zuwa 2002, inda ya samu takardar shedar ilimi ta Najeriya (NCE). Ya yi ritaya daga aikin koyarwa a shekara ta 2012 a matsayin mataimakin shugaban makarantar.[3]

Rigimar doka gyara sashe

Lokacin da Olasunkanmi ya zama Oniroko/Sarki, ya zama shugaban Iroko na farko a sama da shekaru talatin. A baya dai an yi ta cece-kuce kan ko wane ne ya mallaki fili a yankin. Adetunji Kolapo ne ya kawo rikicin shari’a. A wata hira da jaridar Nigerian Tribune a ranar 13 ga Maris 2012, Oniroko ya ce:

"Mutumin ya rubuta takardar koke ga gwamnan jihar Oyo na lokacin, Janar Oladayo Popoola, cewa yana da hakki a kan sarautar Oniroko. Wannan batu dai ya kasance a gaban kotu har na tsawon shekaru 32 kafin daga karshe kotun ta yanke hukuncin a ranar 31 ga watan Janairun 2011 kuma kafin mutumin ya koma kotu, an gabatar da dukkan shaidun da ke nuna cewa an shigar da sabon Oniroko, kamar yadda kotun ta bayyana da umarnin gwamnatin jihar."[3]

Manazarta gyara sashe

  1. Olufemi Atoyebi (April 14, 2015). "Reward For Excellence". TheNation. Retrieved 2015-05-22.
  2. Taiwo Olanrewaju (May 24, 2013). "Traditional ruler solicits Oyo govt's presence at Iroko". NigerianTribune. Retrieved 2015-05-22.
  3. 3.0 3.1 Dapo Falade (March 13, 2012). "Why Iroko was without an Oba for 32 years - Oniroko". NigerianTribune. Archived from the original on 2015-05-18. Retrieved 2015-05-22.