Martin Dominic Martin Hassan (an haife shi a ranar 16 ga watan Satumba 1999) ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Sudan ta Kudu wanda ke taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Ulsan Citizen FC ta Koriya ta Kudu da kuma ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Sudan ta Kudu.

Martin Sawi
Rayuwa
Haihuwa Alexandria, 16 Satumba 1999 (24 shekaru)
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
 
Muƙami ko ƙwarewa Mai buga tsakiya

Aikin kulob gyara sashe

Sawi ya fara aikinsa a kulob din Young Stars na Sudan ta Kudu, [1] kafin ya koma Koriya ta Kudu a shekarar 2016 don shiga kulob ɗin Ansan Greeners. A cikin shekarar 2018, Sawi ya sanya hannu a kungiyar Goyang Citizen. [2] A cikin watan Janairu 2020, bayan ya zira kwallaye 19 a wasanni 35 na Goyang, Sawi ya sanya hannu a kulob din K3 League Yangju Citizen.[3]

Ayyukan kasa da kasa gyara sashe

A watan Nuwamba 2018, Sawi ya buga wasa a tawagar Sudan ta Kudu a 'yan kasa da shekaru 23 da Uganda a filin wasa na Juba. A ranar 17 ga Nuwamba, 2019, Sawi ya fara buga wa Sudan ta Kudu wasa a ci 2-1 da Burkina Faso.[4]

Manazarta gyara sashe

  1. "South Sudanese player signs to South Korean Club" . Hot in Juba. Retrieved 12 December 2019.
  2. "[오피셜] 고양시민축구단, '남수단 네이마르' 마틴 영 입" (in Korean). Naver. 18 May 2018. Retrieved 26 March 2020.
  3. "Sawi Signs For A New Club in The South Korea K3 League" . Kurra Sports. 7 January 2020. Retrieved 26 March 2020.
  4. "South Sudan vs. Burkina Faso" . National Football Teams. Retrieved 26 March 2020.