Lucky Aiyedatiwa

Ɗan siyasar Najeriya

Lucky Orimisan Aiyedatiwa (an haife shi 12 ga Janairu shekarar 1965) ɗan kasuwan Najeriya ne kuma ɗan siyasa wanda ya yi gwamnan jihar Ondo tun 2023.[1][2] Ya taɓa zama mataimakin gwamnan jihar Ondo daga shekarar shekarar 2021 zuwa 2023 a ƙarƙashin tsohon Gwamna marigayi Rotimi Akeredolu. Tsohon kwamishina ne a hukumar raya yankin Neja Delta (NDDC).

Lucky Aiyedatiwa
Deputy Governor of Ondo State (en) Fassara

24 ga Faburairu, 2021 - 27 Disamba 2023
Rayuwa
Haihuwa Ilaje, 12 ga Janairu, 1965 (59 shekaru)
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Lucky Aiyedatiwa

A ranar 12 ga Disamba 2023, Aiyedatiwa ya zama muƙaddashin gwamna bayan tafiyar Gwamna Rotimi Akeredolu yana hutun jinya. Ya taɓa riƙe muƙamin muƙaddashin gwamna daga watan Yuni zuwa Satumba 2023 a lokacin da Akeredolu yake hutun jinya.

Rayuwarsa ta farko gyara sashe

An haifi Aiyedatiwa a ranar 12 ga Janairun shekarar 1965, ya fito ne daga Obe-Nla, al’ummar da ke da arziƙin man fetur a ƙaramar Hukumar Ilaje ta Jihar Ondo.

Manazarta gyara sashe

  1. "Akeredolu, new deputy sworn in for second term". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2021-02-25. Retrieved 2021-04-06.
  2. "'Compete fairly' | The Nation Nigeria". thenationonlineng.net. Retrieved 2022-03-11.