Ƙungiyar Marubuta ta Najeriya ( ANA ) ƙungiya ce mai zaman kanta wacce ke haɓaka adabin Najeriya . Tana wakiltar marubutan Najeriya masu kirkire-kirkire a gida da waje. Marubuci dan Najeriya Chinua Achebe ne ya kafa ta a shekarar 1981 a matsayin shugabanta. [1] [2] Tsohon shugaban na kusa shine Alhaji Denja Abdullahi. Shugaba mai ci shine Camilus Ukah sai kuma mataimakiyar shugaban Hajiya Farida Mohammed . [3]

Kungiyar Marubuta ta Najeriya
writers’ organization (en) Fassara
Bayanai
Farawa 1981

Tarihi gyara sashe

An kafa kungiyar ne a ranar 27 ga watan Yunin 1981 shekaru goma bayan yakin basasar Najeriya, a wani taro a jami'ar Najeriya dake Nsukka . Taron ya samu halartar marubutan Kenya guda biyu, Ngũgĩ wa Thiong'o da Gacheche Wauringi. Bayan haka, Hukumar Kula da Harkokin Kasuwanci ta Najeriya ta yi rajistar kungiyar kamar yadda doka ta yanzu ta 1990 Vide Companies and Allied Matters Act No 1.

Wadanda suka kafa ANA sun hada da Kole Omotoso, Mabel Segun, Ernest Emenyonu, Labo Yari, Femi Osofisan, JP Clark, Niyi Osundare, Jerry Agada da TM Aluko . [4] [5]

Manazarta gyara sashe

  1. "Association of Nigerian Authors". Bambooks.io (in Turanci). Archived from the original on 2020-08-12. Retrieved 2020-05-26.
  2. Edoro, Ainehi (5 November 2013). "Are You A Nigerian Writer? Why Join The Association of Nigerian Authors?--- Brittle Paper Q&A with Richard Ali". Brittle Paper. Retrieved 11 November 2021.
  3. "History | Association of Nigerian Authors". Snanigeria.org. Archived from the original on 7 December 2021. Retrieved 11 November 2021.
  4. Diala (2020). "A Writers' Body and the Nigerian Literary Tradition". Research in African Literatures. 50 (4): 121–141. doi:10.2979/reseafrilite.50.4.08. JSTOR 10.2979/reseafrilite.50.4.08. S2CID 226487570.
  5. "'At 40, we are poised to celebrate our founding fathers'". Thenationonlineng.net. 21 February 2021. Archived from the original on 25 August 2021. Retrieved 11 November 2021.