Katagum

karamar hukuma a jihar Bauchi, Nigeria

Katagum gari ne, ƙaramar hukuma ce kuma ɗaya daga cikin manyan masarautun gargajiya a jihar Bauchi, wace take arewa maso gabashin Najeriya. Garin dai yana bakin kogin Jama’are ne , a arewaci gabar da ruwa, wanda ke gabas da ruwa a Hadejia. Galibin mazauna garin musulmai ƙabilar hausa, itace Mafi rinjaye sai kuma ƙananan kabilu kamar su Fulani da kuma kabilar Kanuri.

Katagum


Wuri
Map
 12°17′00″N 10°21′00″E / 12.2833°N 10.35°E / 12.2833; 10.35
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaJihar Bauchi
Tsarin Siyasa
Majalisar zartarwa supervisory councillors of Katagum local government (en) Fassara
Gangar majalisa Katagum legislative council (en) Fassara
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci
Manyan kayayyakin noma sun haɗa da gyaɗa ( gyada), dawa, gero, shinkafa (musamman a cikin fadama na kogi, ko kuma “filayen ambaliyar ruwa”), da shanu, da auduga, da indigo, da kuma. Dabbobin su sun hada da dawakai, shanu, awaki, tumaki, jakuna da kuma kaji da yawa.

Karamar Hukuma gyara sashe

Garin Katagum shi ne cibiyar gudanar da mulki a ƙaramar hukumar Zaki (LGA). Ƙaramar hukumar Katagum, ƙaramar hukuma ce ta ware kwata-kwata a kudancin karamar hukumar Zaki, wacce ƙaramar hukumar Itas/Gaɗau ta raba ta; Don haka ƙaramar hukumar Katagum ba ta haɗa da garin mai suna; tana da yanki na 1,436 km2 (554 sq mi) da yawan jama'a kusan 295,970 a ƙidayar shekarar 2006; Cibiyar gudanarwar ta ita ce Azare mai yawan jama'a fiye da kashi 50% na daukacin al'ummar Katagum. Lambar gidan waya ita ce 752.