Hassan Shehata ( Larabci: حسن شحاتة ; An haife shi a ranar 19 ga watan Yunin 1947), tsohon ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Masar. Kafin ritaya ya taka leda a matsayin mai tsaron gaba . Daga nan ya zama manajan ƙwallon ƙafa, wanda a yanzu ya yi ritaya. Shehata ya jagoranci ƙasar Masar ta lashe kofuna 3, duka a gasar cin kofin Afrika: 2006, 2008 da 2010. Shi ne koci na farko da ya taɓa lashe kofunan gasar cin kofin Afrika sau uku a jere. Shehata yana daya daga cikin kociyan guda biyu kacal da suka lashe gasar cin kofin Afrika sau 3, tare da Charles Gyamfi na Ghana.[1][2][3]