Brimmo Yusuf
Brimmo Yemi Yusuf ɗan siyasar Najeriya ne. An zaɓe shi Sanata ne na mazaɓar Oyo ta Arewa ta Jihar Oyo, Najeriya a farkon Jamhuriya ta huɗu ta Najeriya, yana gudana a kan tsarin Alliance for Democracy (AD). Ya hau mulki a ranar 29 ga watan Mayun shekarar 1999.
Brimmo Yusuf | |||
---|---|---|---|
Mayu 1999 - Mayu 2003 - Robert B. Koleoso → District: Oyo North | |||
Rayuwa | |||
Haihuwa | Oyo, | ||
ƙasa | Najeriya | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa da soja | ||
Imani | |||
Jam'iyar siyasa |
Peoples Democratic Party Alliance for Democracy (en) |
Brimmo Birgediya Janar ne mai ritaya. Tsohon daliɓi ne a Cibiyar Nazarin Manufofin Najeriya da Nazari. Ya riƙe muƙamai daban-daban a cikin Sojoji ciki har da Muƙaddashin Janar ɗin Kwamanda mai ritaya ta 82. Daga shekarata 1996 zuwa 1999 ya kasance darakta a kamfanin Odu’a Investment Company Limited. Bayan ya hau kujerarsa ta majalisar dattijai a cikin watan Yunin shekarata 1999 an naɗa shi kwamitocin kan harkokin cikin gida, tsaro da kuma leken asiri, tsaro da kuma fataucin miyagun kwayoyi. ). Brimmo ya koma PDP a shekarar 2001, kuma a cikin watan Nuwamban shekarar 2002 ya kasance mai hankoron zama Gwamnan jihar Oyo a ƙarƙashin jam'iyyar PDP.
A cikin watan Nuwamba na shekarar 2009 aka naɗa Brimmo a matsayin Shugaban Kamfanin saka jari na Odu’a.
Manazarta gyara sashe
https://web.archive.org/web/20090424083701/http://www.oduainvestmentcompany.com/boardDir.htm