Benard E. Aigbokhan
Benard E. Aigbokhan malami ne ɗan ƙasar Najeriya, (an haife shi a ranar 3 ga watan Oktoba, 1951) kuma masani ne kan harkokin tattalin arziki.[1] Ya yi aiki a matsayin mataimakin shugaban jami'ar Samuel Adegboyega, Nigeria daga ranar 7 ga watan Janairu, 2013 zuwa ranar 6 ga watan Janairu, 2020.
Benard E. Aigbokhan | |
---|---|
Rayuwa | |
Haihuwa | Ewu (en) , 3 Oktoba 1952 (71 shekaru) |
ƙasa | Najeriya |
Karatu | |
Makaranta |
University of the West of Scotland (en) University of Paisley (en) |
Sana'a | |
Sana'a | Malami da Mai tattala arziki |
Rayuwar farko gyara sashe
An haifi Eronmonsele a Ewu Ishan, Edo, Nigeria ɗa ne ga dangin David Ikhifa da Comfort Otiti Aigbokhan a ranar 3 ga watan Oktoba, 1952. A cikin shekarar 1978 ya sami digirinsa a fannin tattalin arziki a Jami'ar Gabashin London, Ingila, da Master of science a fannin tattalin arziki a Jami'ar Stirling, Scotland, 1979. PhD a fannin tattalin arziki ya zo a Jami'ar Yammacin Scotland, tsohuwar Jami'ar Paisley, Scotland, Aa shekarar 1985.[2]
Sana'a gyara sashe
Eronmonsele ya fara aikinsa ne a matsayin babban jami'i a ma'aikatar yaɗa labarai ta tarayya, jihar Legas daga shekarun 1972 zuwa 1973. Daga nan, ya tafi Scotland kuma ya yi aiki a matsayin mataimakin mai koyarwa a Jami'ar Paisley daga shekarun 1982 zuwa 1985. Bayan haka, ya dawo Najeriya ne a matsayin malami a Jami’ar Jihar Imo a shekarar 1986 sannan ya wuce Jami’ar Jihar Edo, Ekpoma, daga shekarun 1987 zuwa 1992 a matsayin mai karatu. Ya zama farfesa a fannin tattalin arziki a shekarar 1995. Daga baya ya zama ma’aikacin Resource na kwamitin UNESCO na ƙasa a jihar Legas daga shekarun 1989 zuwa 1991 da cibiyar kula da harkokin tattalin arziki da gudanar da mulki a Ibadan, Najeriya, tun daga shekarar 1991.[3]
Ayyuka gyara sashe
Eronmonsele ya yi rubutu akan Tsare-tsare, Aiki da Rarraba Kuɗi a Najeriya a cikin shekarar 1988. Ya yi rubutu akan Ka'idar Macroeconomic, Policy and Evidence a cikin shekarar 1995. Ya yi aiki a matsayin Edita na Iroro Journal of Arts and Social Sciences daga shekarun 1987 zuwa 1992. Ya kasance Mai Ba da Gudunmawa a Global visions: Beyond New World Order a shekarar 1993. Ya rubuta ayyuka 13 a cikin littattafai 23 a cikin yare 1. Ya kuma halarci tare da gabatar da kasidu a yawancin tarurrukan ilimi.[4]
Rayuwa ta sirri gyara sashe
Eronmonsele ya auri Fummilayo Ogedengb a ranar 3 ga watan Agusta, 1985. Sun rabu a watan Nuwamba 1988. Ya auri Rita Ekhuelohan Atoe a ranar 2 ga watan Janairu, 1991 kuma yana da 'ya'ya 3.[5]
Manazarta gyara sashe
- ↑ "ANEEJ mourns Board Chairman, Prof Aigbokhan". Vanguard News (in Turanci). 2020-07-14. Retrieved 2022-03-04.
- ↑ "SAU ORGANISES INTERNATIONAL CONFERENCE IN HONOUR OF PROFESSOR BENARD AIGBOKHAN – SAU News" (in Turanci). Archived from the original on 2022-11-28. Retrieved 2022-11-28.
- ↑ "Bernard Eronmonsele Aigbokhan Archives". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). Archived from the original on 2022-11-28. Retrieved 2022-11-28.
- ↑ "UNN Staff Profile". www.unn.edu.ng. Retrieved 2022-11-28.
- ↑ "UNN Staff Profile". www.unn.edu.ng. Retrieved 2022-11-28.