Abdelkrim Ghallab (31 ga Disamba, 1919 - 14 ga Agusta, 2017) ɗan jaridar Maroko ne ɗan siyasa, mai sharhi kan al'adu, kuma marubuci. An haifeshi a Fes, Morocco. Ya kasance muhimmin mutum a fagen adabi da siyasa. Yayi karatunsa duka a Jami'ar Al-Karaouine da ke Fez da kuma ta Alkahira .

Abdelkrim Ghallab
Rayuwa
Haihuwa Fas, 31 Disamba 1919
ƙasa Moroko
Mutuwa Casa Blanca (en) Fassara, 14 ga Augusta, 2017
Karatu
Makaranta Cairo University (en) Fassara
Jami'ar al-Karaouine
Harsuna Larabci
Sana'a
Sana'a ɗan jarida da marubuci
Mamba Academy of the Kingdom of Morocco for Royaume (en) Fassara
Imani
Jam'iyar siyasa Istiqlal Party (en) Fassara
Abdelkrim Ghallab

Ghallab shi ne marubucin littattafai biyar da tarin gajerun labarai. Babban sanannen labarinsa shine Dafann al-m'd (Wanda aka binne a baya), 1966. A cewar Simon Gikandi salon sa na larabci an san shi da "kyakkyawa kuma a wasu lokutan ilimin gargajiya". [1]

A cikin 2000, Haɗaɗɗiyar marubutan Larabawa a Misira sun haɗa da littafinsa mai suna Al-Mu`alîm `Ali (Master Alí) daga cikin ingantattun litattafan Larabci guda 100 a tarihi. A cikin 2001, sashen Al'adu na Maroko ya buga cikakken aikin Ghallab cikin mujalladai biyar. A cikin 2004 an ba shi lambar yabo ta Maghreb na Tunis . An fassara aikinsa a cikin harsuna da yawa. [2]

Ghallab ya mutu a El Jadida a ranar 14 ga Agusta, 2017, yana da shekara 97. [3]

Manazarta gyara sashe

  1. Simon Gikandi, Encyclopedia of African literature, p. 283
  2. Salim Jay, Dictionnaire des écrivains marocains, Casablanca: Eddif, 2005, p. 191
  3. "Le journaliste et écrivain marocain Abdelkrim Ghallab est décédé" Archived 2017-11-09 at the Wayback Machine In: huffpostmaghreb.com, Retrieved 14 August 2017]