Uzamat Akinbile Yussuf wacce aka fi sani da Uzamat Folashayo Akinbile Yussuf (an haife ta a shekara ta 1976),[1] Ita mai harhaɗa magunguna ce (pharmacist), mai kare hakkin matasa, ’yar siyasa, kuma mai son taimakon al'umma.[2] Ita ce kwamishina a yanzu haka a Ma’aikatar Yawon Buɗe Ido ta Jihar Legas, an canza matsayinta daga Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida na Jihar Legas zuwa ta Ma'aikatar bude ido (Torism) na Jihar Legas.[3][4][5]

Uzamat Akinbile Yussuf
Rayuwa
Haihuwa 1976 (47/48 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Jami'ar Lagos 2006)
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Ilimi gyara sashe

Ta halarci makarantar firamare ta Ansar-ud-deen Primary School, Ile ife a tsakanin shekarar 1980 zuwa 1986. Daga baya, ta sami shiga cikin makarantar Seventh Day Adventist Grammar, Ile Ife tsakanin 1987 da 1992. Ta samu shiga Jami’ar Lagos, inda ta kammala a shekara ta 2006.[2] Ta kasance memba na kungiyar masu hada Magungunanwato Association of Ladies Pharmacists Society (ALPS), da kuma kungiyar Social Workers of Nigeria (NASOW) da kuma kungiyar Pharmacists Society of Nigeria.[3] Ta buga wani littafi mai suna Duty Calls.[3][6]

Rayuwar mutum gyara sashe

Tana da aure da yara.

Manazarta gyara sashe

  1. "Ogunleye, Titilope (2019-06-17). "LAGOS Commissioner, Pharm AKINBILE-YUSSUF, Celebrates 45th Birthday In Style". City People Magazine. Retrieved 2020-11-11.
  2. 2.0 2.1 "HON. MRS UZAMAT AKINBILE YUSSUF-HONOURABLE COMMISSIONER". Ministry Of Wealth Creation And Employment – Lagos State Government. Retrieved 2020-11-11.
  3. 3.0 3.1 3.2 "Lagos State reshuffles cabinet, appoints Akinbile-Yusuf tourism commissioner". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2020-01-18. Retrieved 2020-11-11.
  4. "Ex-Lagos commissioner launches book on stewardship". Latest Nigeria News, Nigerian Newspapers, Politics (in Turanci). 2019-06-22. Retrieved 2020-11-11.
  5. "Akomolafe, Jesutomi (2019-06-18). "Nigeria: Ex-Lagos Commissioner Marks Birthday With Book Launch On Stewardship". allAfrica.com. Retrieved 2020-11-11.
  6. "Ex-Lagos commissioner launches book on stewardship". Latest Nigeria News, Nigerian Newspapers, Politics (in Turanci). 2019-06-22. Retrieved 2020-11-11.