Rachid Ghaflaoui (Larabci: رشيد الغفلاوي; an haife shi ranar 1 ga watan Janairun 1973) kocin ƙwallon ƙafa ne na ƙasar Morocco. Shi ne kocin kulob ɗin Al Ta'awon SC na ƙasar Libya a yanzu wanda ke taka leda a gasar cin kofin Libya. [1]

Rachid Ghaflaoui
Rayuwa
Haihuwa Marrakesh, 1 ga Janairu, 1973 (51 shekaru)
ƙasa Moroko
Sana'a

Sana'a gyara sashe

An haife shi a Marrakech a Maroko, Ghaflaoui an naɗa shi a 2014 a matsayin kocin ƙungiyar Sahel SC ta Nijar, kafin ya koma ƙungiyar Sanga Balende ta Congo a cikin watan Fabrairun 2016, wanda ya yi nasarar samun tikitin shiga gasar cin kofin Confederation [2] ta hanyar kammala matsayi na uku a gasar zakarun Congo.

A cikin watan Nuwambar 2017, ya sake ƙulla yarjejeniya da ƙungiyar Sahel SC ta Nijar, kulob ɗin da ya lashe kofin ƙasar da Supercup a kakar wasa guda, kafin ya ƙulla yarjejeniya da kulob ɗin Williamsville Athletic Club na Ivory Coast a kakar wasa ta gaba.

A cikin shekarar 2020, ya shiga kulob ɗin Guinean Académie SOAR, [3] sannan a cikin 2021, kulob ɗin Bahrain SC na Bahrain wanda tare da shi zai sami ci gaba zuwa gasar Premier ta Bahrain. [4]

Girmamawa gyara sashe

  • Kofin Niger: 2017
  • Super Cup: 2017
  • Zakaran Bahrain Dision na Biyu: 2022

Manazarta gyara sashe

  1. Rachid Ghaflaoui débarque à Taawon SC Archived 2022-09-07 at the Wayback Machine AfricaFootUnited
  2. "Ses choix de carrière, ses bons et mauvais souvenirs". Archived from the original on 2022-09-08. Retrieved 2023-03-25.
  3. Les coachs arabes : La nouvelle génération
  4. غفلاوي يبلغ صدارة الدوري البحريني Hespress