Ned Charles (an haife shi a ranar 28 ga watan Mayun shekarar 1957 a Mahébourg) tsohon ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Mauritius wanda ya taka leda a matsayin ɗan wasan gaba. Ya kuma wakilci tawagar kasar Mauritius sau tara, inda ya zura kwallo daya.[1]

Ned Charles
Rayuwa
Haihuwa Mahébourg (en) Fassara, 28 Mayu 1957 (66 shekaru)
ƙasa Moris
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
  Mauritius national football team (en) Fassara-
R. Wallonia Walhain Chaumont-Gistoux (en) Fassara-
Union Royale Namur (en) Fassara-
Le Puy Foot 43 Auvergne (en) Fassara-
  Cercle Brugge K.S.V. (en) Fassara1979-198020
 
Muƙami ko ƙwarewa Ataka

Charles ya shafe yawancin aikinsa a Belgium, bayan kungiyar kwallon kafa ta Cercle Brugge ta gano shi. Ko da yake zai zauna na kakar wasa daya kawai kuma ya buga wasa sau biyu a gefen kore da baki, ya zauna a yankin Bruges.[2] A ƙarshen aikinsa na wasa, Charles ya zama kocin matasa na ƙungiyar SV Oostkamp na gida kuma a cikin wani mataki na gaba Cercle Brugge da VV-Emelgem-Kachtem.

Bayan wani lokaci a Faransa tare da kungiyar kwallon kafa ta USF Le Puy, Charles ya koma Belgium, ya ƙare aikinsa tare da ƙungiyoyi biyu na Walloon: UR Namur da Wallonia Walhain.[3]

Manazarta gyara sashe

  1. Cerclemuseum.be (in Dutch)
  2. Hydoo, Azmaal (2 January 2018). "Ned Charles: « S'inspirer de l'Ajax Amsterdam pour relancer le football mauricien»" . L'Express (in French). Retrieved 1 May 2020.
  3. "Ned Charles, un Mauricien au service du foot belge" . L'Express (in French). 20 May 2004. Retrieved 1 May 2020.