Muhammad Jibrin wanda aka fi sani da Dan Barde ɗan siyasar Najeriya ne kuma dan kasuwa daga jihar Gombe. Ya kasance tsohon dan takarar gwamna na jam'iyyar All Progressives Congress a 2019 kuma dan takarar PDP na yanzu na zaben 2023.

Muhammad Barde

Ya kasance Babban Jami’in Bankin Sun Trust, Mataimakin Shugaban Kungiyar Masu Bayar da Lamuni ta Najeriya na Kasa, Darakta na Premium Pensions Limited, Daraktan Hukumar Fasaha ta Hukumomin Gidajen Tarayya da kuma memba a Kwamitin Shugaban Kasa kan Gidaje masu araha.

Manazarta

gyara sashe