Fadwa Abd al-Rahman Ali Taha ( Larabci: فدوى عبد الرحمن علي طه‎; An haife ta a ranar 23 ga watan Oktoba 1955 a Arbaji, Jihar Gezira, Sudan) farfesa ce a Sashen Tarihi, a Jami'ar Khartoum. [1]

Fadwa Taha
vice dean (en) Fassara

2007 -
Rayuwa
Haihuwa Arbaji (en) Fassara, 23 Oktoba 1955 (68 shekaru)
ƙasa Sudan
Karatu
Makaranta University of Khartoum (en) Fassara
University of Bergen (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Tarihin Rayuwa gyara sashe

Rayuwar farko da ilimi gyara sashe

An haifi Fadwa Abd al-Rahman Ali Taha a Arbaji, Jihar Gezira, a ranar 23 ga watan Oktoba 1955, kuma ta girma a can. Ta kasance ƙwararriyar masaniyar tarihi wacce ta sami digiri na farko a fannin fasaha a shekarar 1979, Master of Arts a shekarar 1982, PhD a shekarar 1987, duk daga Jami'ar Khartoum. Daga baya ta sami Master of Art a fannin fassara, a cikin shekarar 2002, ban da digiri na girmamawa daga Jami'ar Bergen a Norway a shekarar 2004.[2]

Sana'a gyara sashe

Fadwa ta shiga Jami’ar Khartoum a matsayin mataimakiyar mai koyarwa a shekarar (1979), ta zama malama a shekarar (1997) mataimakiyar farfesa a shekarar (1992) mataimakiyar farfesa a shekarar 2000 sannan ta zama cikakkiyar farfesa a shekarar 2012. A shekara ta 2010, ta zama editan Jaridar Faculty of Arts a Jami'ar Khartoum, kuma an naɗa ta a matsayin Shugabar Sashen Tarihi. A shekarar 2007, ta zama mataimakiyar shugaban tsangayar karatun digiri.[3] Daga baya ta koma Saudi Arabiya kuma a shekara ta 2010 don zama alhakin inganci, bincike da nazarin kimiyya a Kwalejin Ilimi a Hafr Al-Batin.[4] An naɗa ta shugabar Jami'ar Khartoum a watan Oktobar 2019.[5]

Fadwa ta shiga cikin juyin juya halin Sudan a shekarar 2019, wanda ya kawo karshen gwamnatin Omar al-Bashir. Ta kuma taka rawa a tattaunawar da aka yi tsakanin dakarun 'yanci da sauyi da majalisar soji, wacce ta maye gurbin gwamnatin al-Bashir jim kaɗan bayan juyin mulkin. Majalisar rikon kwarya ta kasa ce ke jagorantar kasar a lokacin rikon kwarya har sai an shirya wani sabon zabe da kuma kafa zababbiyar gwamnati. Bayan da bangarorin biyu suka cimma matsaya guda a ranar 5 ga watan Yuli 2019.[6] An gayyace ta ta shiga majalisar amma ta ki. [7]

Ta yi murabus a watan Nuwamba 2021 don nuna adawa da yarjejeniyar maido da Abdalla Hamdok a matsayin Firayim Minista bayan juyin mulkin Sudan na 2021.[8]

Rayuwa ta sirri gyara sashe

Fadwa tana auren Al-Miqdad Ahmed Ali kuma suna da ‘ya’ya biyu; Hatem, wanda ya yi karatu a School of Administrative Sciences, Jami'ar Khartoum, da Ezzat, wanda ya kammala karatunsa a Sashin Lantarki a jami'a guda.[9]

Manazarta gyara sashe

  1. ﺍﻟﺒﺮﻭﻓﻴﺴﻮﺭ ﻓﺪﻭﻯ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻋﻠﻲ ﻃﻪ" . 02-04-2018 . Archived from the original on 2019-05-19. Retrieved 2019-07-07.
  2. ﻓﺪﻭﻯ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻋﻠﻲ ﻃﻪ : ﺃﻭﻝ ﺳﻴﺪﺓ ﺗﺤﻤﻞ ﻟﻘﺐ ﺍﻷﺳﺘﺎﺫﻳﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﺭﺍﺳﺎﺕ ﺍﻹﻧﺴﺎﻧﻴﺔ ﻣﻦ ﺟﺎﻣﻌﺔ ﺍﻟﺨﺮﻃﻮﻡ " . Archived from the original on 2019-07-07. Retrieved 2019-07-07.
  3. " ﺗﻜﺮﻳﻢ ﺍﻟﺒﺮﻭﻑ ﻓﺪﻭﻯ ﻋﺒﺪﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻋﻠﻲ ﻃﻪ ﺷﺨﺼﻴﺔ ﺍﻟﺴﻮﺩﺍﻥ ﺍﻟﺜﻘﺎﻓﻴﺔ ﻭﻟﻘﺎﺀ ﻣﻌﻬﺎ " . Archived from the original on 2019-12-10. Retrieved 2019-07-07.
  4. ﺍﻟﺒﺮﻭﻓﺴﻴﺮ ﻓﺪﻭﻯ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻋﻠﻲ ﻃﻪ : ﺛﻮﺭﺓ ﺍﻟﺘﻌﻠﻴﻢ ﺍﻟﻌﺎﻟﻲ ﻛﺎﺭﺛﺔ " . Archived from the original on 2017-08-11. Retrieved 2019-07-07.
  5. "Sudan (University of Khartoum) The President of the University of Khartoum receives the Chairman of the Board of Trustees of the Arab International Center for Entrepreneurship – SDGS UNIVERSITIES" . Retrieved 2023-06-22.
  6. " ﺑﺎﻷﺳﻤﺎﺀ ﻭﺍﻟﻤﻨﺎﺻﺐ .. ﺍﻟﺠﺰﻳﺮﺓ ﻧﺖ ﺗﻜﺸﻒ ﺗﻔﺎﺻﻴﻞ ﺍﻟﺘﺮﺷﻴﺤﺎﺕ ﻟﻤﺠﻠﺴﻲ ﺍﻟﺴﻴﺎﺩﺓ ﻭﺍﻟﻮﺯﺭﺍﺀ ﻓﻲ ﺍﻟﺴﻮﺩﺍﻥ " . www.aljazeera.net . Archived from the original on 2019-07-06. Retrieved 2019-07-07.
  7. SudanTribune (2019-08-17). "FFC delay announcement of nominees for Sudan's Sovereign Council" . Sudan Tribune . Retrieved 2023-06-22.
  8. "Director of the University of Khartoum resigns in protest of the Burhan-Hamdok agreement" . Middle East Monitor . 2021-11-22. Retrieved 2023-06-22.
  9. ﺩ / ﻓﺪﻭﻯ ﻋﺒﺪﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻋﻠﻲ ﻃﻪ " . arbaji.org . Archived from the original on 10 December 2019.