Emueje Ogbiagbevha yar wasan kwallon kafa ce ta Najeriya da ke taka leda yanzu haka a kungiyar kwallon kafa ta FC Minsk a gasar Premier ta Belarusiya . Ta taba buga wa BIIK Kazygurt a Gasar Kazakhstani, [1] da kuma Gasar Rasha ta Rossiyanka da Energiya Voronezh. Ita ce ta fi kowa zira kwallaye a kakar 2010 yayin da take wasa a Rossiyanka, wanda da ita ta samu nasara biyu. Ta kuma buga Kofin Zakarun Turai tare da Energiya Voronezh da Kazygurt, kuma ita memba ce a kungiyar kwallon kafa ta Nijeriya. Yarjejeniyarta da BIIK Kazygurt ta ƙare a ƙarshen shekarar 2012.  [ bukatar sabuntawa ] A cikin shekara ta 2016, Ogbiagbevha ta koma FC Minsk . ta buga kwallo a nasarawa da delta yayin tasowarta.

Emueje Ogbiagbevha
Rayuwa
Haihuwa Warri, 10 ga Faburairu, 1990 (34 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
Pelican Stars F.C. (en) Fassara2006-2007
  Nigeria women's national under-20 football team (en) Fassara2006-200610
WFC Rossiyanka (en) Fassara2008-201029
FC Energy Voronezh (en) Fassara2011-20121315
  Kungiyar kwallon kafa ta mata ta Najeriya2012-
BIIK Kazygurt (en) Fassara2012-2012
FC Minsk (mata)2016-20205279
 
Muƙami ko ƙwarewa Ataka
Tsayi 1.75 m

A cikin kakar shekarar 2019 zuwa 2020 ta zama matan Afirka na farko da suka ci kyautar (raba) UEFA Champions League ta mata mafi girma. [2] Bayan kakar wasanni kwangilarta ta kare a Minsk. [3]

Farkon aiki gyara sashe

Ta taba taka leda a Pelican Stars FC, Nasarawa Amazons da Delta Queens FC a gasar Firimiyar Nigeria ta Mata .

Manazarta gyara sashe